• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Girgizar Kasar Maroko Da Ambaliyar Ruwar Libiya: Sama Da Rayuka 8,000 Sun Salwanta

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Libiya

A ‘yan kwanakin nan ne al’uimmar duniya suka tashi da wata mummunan girgizar kasar da aka dade ba a ga irinta ba a kasar Moroko inda zuwa yanzu aka tabbatar da mutuwar mutum fiye da 3,000, duk da wasu da dama na kwance a asibitoci ana kuma ci gaba da zakulo mutanen da suka makale a baraguzan gine-ginen da suka dannesu.

Wani abin al’ajabi a na kuma shi ne yadda al’umma duniya suka hadu wajen jajatanwa tare da kai agajin gaggwa don tallafa wa wadanda suka jikkata da kuma bayar da taimakon gaggawa ga wadanda suka tsira.
Gidan talbijin na Moroko, wanda ya ambato ma’aikatar harkokin cikin gida ta kasar tana bayyana haka, ya kara da cewa a kididdigkr fkro mutum 672 ne suka jikkata sakamakon girgizar kasar mai karfin maki 7.0 da ta kassara yankuna da dama na kasar.

  • Sin Na Bin Diddigin Hasarar Rayuka Da Dukiyoyi Da Mahaukaciyar Guguwa Ta Haddasa A Gabashin Libya

Girigizar kasar ta kuma lalata gine-gine yayin da mutane suka rika tserewa daga gidajensu cikin firgici.

“Rahoton wucin-gadi ya nuna cewa girgizar kasar ta kashe fiye da mutum 3000 a larduna da biranen al-Haouz, Marrakesh, Ouarzazate, Azilal, Chichaoua da kuma Taroudant,” in ji sanarwar, wadda ta kara da cewa an garzaya da wadanda suka jikkata zuwa asibiti.

Wasu bidiyoyi da aka rika watsawa a shafukan sada zumunta wadanda ba a tantance sahihancinsu ba sun nuna yadda gine-gine suka rika rushewa yayin da wasu suke girgiza. An ga mutane cikin dimuwa yayin da wasu suke fitowa daga baraguzan gine-gine.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

“Mun ji wata mahaukaciyar girgiza. Daga nan na fahimci cewa girgizar kasa ce. Mutane sun fada cikin firgici da yamutsi. Yara suna ta kuka yayin da iyaye suka dimauce,” kamar yadda Abdelhak El Amrani, wani mazaunin Marrakesh ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP ta wayar tarho.

Hukumar da ke nazari kan girgizar kasa ta Amurka [USGS] ta ce bayanan farko sun nuna cewa girgizar kasar da ta auku a Maroko tana da karfin maki 6.8 kuma ta faru a nisan kilomita 18 daga karkashin kasa.
Ta ce girgizar kasar ta faru ne da misalin karfe 11:11 na dare a agogon kasar kuma ta fi kamari a yanki mai fadin kilomita 56.3 a yammacin Oukaimeden, fitaccen wurin yin wasan zamiya da ke Tsaunukan Atlas.
Kafofin watsa labaran Maroko sun ce girgizar kasar ita ce mafi karfi da kasar ta taba fuskanta a tarihinta.

An ji karar girgizar kasar a Algeria da ke makwabtaka da Maroko, ko da yake Jami’an Tsaron Algeria sun ce ba ta yi wata barna ba.
A 2004, akalla mutum 628 ne suka mutu yayin da 926 suka jikkata sakamakon girgizar kasar da ta auku a Al Hoceima da ke arewacin Maroko.

Zuwa yanzu ana ci gaba da bayar da agaji kayan abinci da magunguna don, ana kuma ci gaba da zakulo wasu daga cikin baraguzan gine-ginen.

Ana cikin wannan alhinin ne kuma labarin wata mummuna ambaliyar ruwa da guguwar da ta ratsa kasar Libiya ta ruiski al’umma duniya, inda ita ma zua yanzu aka yi asarar rayukar mutane da duniyoyi na biliyoyn daloli.

Shugabannin duniya sun mika sakon jaje ga al’umma kasar, cikin na gaba-gaba a mika sakon jajen shi ne shugaban kasa Sin Di Jinping ya mika sakon jejen ga Mohamed Menfi, shugaban majalisar gudanarwar Libya, dangane da mahaukaciyar guguwar da ta afkawa kasar Libya.

A cikin sakon nasa, shugaba Di ya ce, ya kadu matuka da samun labarin mahaukaciyar guguwar da ta afkawa kasar, lamarin da ya janyo hasarar rayuka da dukiyoyi.

A madadin gwamnati da al’ummar Sinawa, Di ya yi jimami matuka ga wadanda abin ya shafa, tare da nuna jaje ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da ma wadanda suka jikkata. Haka kuma shugaba Di ya bayyana imaninsa cewa, ko shakka babu al’ummar Libya za su shawo kan illar iftila’in.

Ma’aikatar lafiya ta Libiya ta bayyana yau cewa, akalla mutane fiye da 5, 000 ne suka mutu yayin da sama da dubu biyar suka bace a birnin Derna na kasar, bayan da wata mummunar ambaliyar ruwa da ta mamaye gabashin kasar a ranar Lahadin da ta gabata.
Haka kuma a halin yanzu kasashen duniya na ci gaba da kai kayyakin agaji na abin da magunguna ga al’umma kasar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC
Labarai

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi
Manyan Labarai

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Next Post
Sin

Gwamnatin Sin Ta Yanke Shawarar Baiwa Libya Tallafin Jin Kai Na Gaggawa

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.