• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Girgizar Kasar Maroko Da Ambaliyar Ruwar Libiya: Sama Da Rayuka 8,000 Sun Salwanta

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Libiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ‘yan kwanakin nan ne al’uimmar duniya suka tashi da wata mummunan girgizar kasar da aka dade ba a ga irinta ba a kasar Moroko inda zuwa yanzu aka tabbatar da mutuwar mutum fiye da 3,000, duk da wasu da dama na kwance a asibitoci ana kuma ci gaba da zakulo mutanen da suka makale a baraguzan gine-ginen da suka dannesu.

Wani abin al’ajabi a na kuma shi ne yadda al’umma duniya suka hadu wajen jajatanwa tare da kai agajin gaggwa don tallafa wa wadanda suka jikkata da kuma bayar da taimakon gaggawa ga wadanda suka tsira.
Gidan talbijin na Moroko, wanda ya ambato ma’aikatar harkokin cikin gida ta kasar tana bayyana haka, ya kara da cewa a kididdigkr fkro mutum 672 ne suka jikkata sakamakon girgizar kasar mai karfin maki 7.0 da ta kassara yankuna da dama na kasar.

  • Sin Na Bin Diddigin Hasarar Rayuka Da Dukiyoyi Da Mahaukaciyar Guguwa Ta Haddasa A Gabashin Libya

Girigizar kasar ta kuma lalata gine-gine yayin da mutane suka rika tserewa daga gidajensu cikin firgici.

“Rahoton wucin-gadi ya nuna cewa girgizar kasar ta kashe fiye da mutum 3000 a larduna da biranen al-Haouz, Marrakesh, Ouarzazate, Azilal, Chichaoua da kuma Taroudant,” in ji sanarwar, wadda ta kara da cewa an garzaya da wadanda suka jikkata zuwa asibiti.

Wasu bidiyoyi da aka rika watsawa a shafukan sada zumunta wadanda ba a tantance sahihancinsu ba sun nuna yadda gine-gine suka rika rushewa yayin da wasu suke girgiza. An ga mutane cikin dimuwa yayin da wasu suke fitowa daga baraguzan gine-gine.

Labarai Masu Nasaba

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

“Mun ji wata mahaukaciyar girgiza. Daga nan na fahimci cewa girgizar kasa ce. Mutane sun fada cikin firgici da yamutsi. Yara suna ta kuka yayin da iyaye suka dimauce,” kamar yadda Abdelhak El Amrani, wani mazaunin Marrakesh ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP ta wayar tarho.

Hukumar da ke nazari kan girgizar kasa ta Amurka [USGS] ta ce bayanan farko sun nuna cewa girgizar kasar da ta auku a Maroko tana da karfin maki 6.8 kuma ta faru a nisan kilomita 18 daga karkashin kasa.
Ta ce girgizar kasar ta faru ne da misalin karfe 11:11 na dare a agogon kasar kuma ta fi kamari a yanki mai fadin kilomita 56.3 a yammacin Oukaimeden, fitaccen wurin yin wasan zamiya da ke Tsaunukan Atlas.
Kafofin watsa labaran Maroko sun ce girgizar kasar ita ce mafi karfi da kasar ta taba fuskanta a tarihinta.

An ji karar girgizar kasar a Algeria da ke makwabtaka da Maroko, ko da yake Jami’an Tsaron Algeria sun ce ba ta yi wata barna ba.
A 2004, akalla mutum 628 ne suka mutu yayin da 926 suka jikkata sakamakon girgizar kasar da ta auku a Al Hoceima da ke arewacin Maroko.

Zuwa yanzu ana ci gaba da bayar da agaji kayan abinci da magunguna don, ana kuma ci gaba da zakulo wasu daga cikin baraguzan gine-ginen.

Ana cikin wannan alhinin ne kuma labarin wata mummuna ambaliyar ruwa da guguwar da ta ratsa kasar Libiya ta ruiski al’umma duniya, inda ita ma zua yanzu aka yi asarar rayukar mutane da duniyoyi na biliyoyn daloli.

Shugabannin duniya sun mika sakon jaje ga al’umma kasar, cikin na gaba-gaba a mika sakon jajen shi ne shugaban kasa Sin Di Jinping ya mika sakon jejen ga Mohamed Menfi, shugaban majalisar gudanarwar Libya, dangane da mahaukaciyar guguwar da ta afkawa kasar Libya.

A cikin sakon nasa, shugaba Di ya ce, ya kadu matuka da samun labarin mahaukaciyar guguwar da ta afkawa kasar, lamarin da ya janyo hasarar rayuka da dukiyoyi.

A madadin gwamnati da al’ummar Sinawa, Di ya yi jimami matuka ga wadanda abin ya shafa, tare da nuna jaje ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da ma wadanda suka jikkata. Haka kuma shugaba Di ya bayyana imaninsa cewa, ko shakka babu al’ummar Libya za su shawo kan illar iftila’in.

Ma’aikatar lafiya ta Libiya ta bayyana yau cewa, akalla mutane fiye da 5, 000 ne suka mutu yayin da sama da dubu biyar suka bace a birnin Derna na kasar, bayan da wata mummunar ambaliyar ruwa da ta mamaye gabashin kasar a ranar Lahadin da ta gabata.
Haka kuma a halin yanzu kasashen duniya na ci gaba da kai kayyakin agaji na abin da magunguna ga al’umma kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Girgizar KasaLibyaMorocco
ShareTweetSendShare
Previous Post

Amurka Ba Ta Da Ikon Sukar Sin Game Da Yaduwar Miyagun Kwayoyi

Next Post

Gwamnatin Sin Ta Yanke Shawarar Baiwa Libya Tallafin Jin Kai Na Gaggawa

Related

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

1 hour ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

2 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

10 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

11 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

12 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

14 hours ago
Next Post
Sin

Gwamnatin Sin Ta Yanke Shawarar Baiwa Libya Tallafin Jin Kai Na Gaggawa

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.