• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobara Ta Hallaka Yara Biyu A Madina Kwatas Da Ke Bauchi

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Gobara

Al’ummar unguwar Madina Kwatas sun tashi da mummunar ibtila’in gobara wacce ta yi sanadin rasa yara kanana biyu – Zainab Bashir Muhammad (Hibba) mai shekara 7 da kuma Ummu Salma Bashir (Afnan) mai shekara 5 a duniya.

Gobarar wacce ta tashi a makwabtar wakilinmu da ke unguwar Madina quarters a kusa da makarantar Barden Gabas da ke yankin Turwun, ya rahoto cewa, gobarar ta tashi ne da misalin karfe 11 na safiyar ranar Lahadi.

  • Rukunin Farko Na Masu Yawon Bude Ido Da Suka Samu Bizar Tashar Shige Da Fice Ya Isa Xinjiang
  • Dokar Masana’antar Fetur (PIB): Yadda Aka Yi Wa Kudin Man Fetur Kofar-raggo A Nijeriya

Abun da ya faru kuwa shi ne, mahaifiyar yaran ta fita unguwa inda ta bar yaranta biyu a cikin daki bayan ta kulle dakin tare da kofar gida.

“Lokacin da muka ji wutar ta tashi mun nufi gidan ni da makwabtana, mun yi duk kokarin balle kofar gidan amma hakan ya cutura sai da aka nemo guduma aka balle. Ana wannan gabar, mun yi kokarin haurawa gidan ta sama, inda muka tarar da wutar ci karfin dakin da yaran suke.

“Bayan shiganmu cikin gidan, mun yi kokarin balle kofar dakin amma hakan ba ta yiwu ba. Wuta ce sosai da hayaki mai illa matuka,” In ji wakilinmu da lamarin ya wakana a kan idonsa.

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Kazalika, Usman Abdullahi (Dan Usmanu) ya shaida cewar, “Allah dai ya aiko da tsautsayi amma ba dabi’ar matar ba ne kulle yara a gida. Wani lokacin in za ta fita ta na kawo yaranta gidana saboda gidan na kusa da kofar gidana.

“Mijinta mai suna Bash baya nan a lokacin da wutar ta tashi. Har yanzu dai ba mu gano hakikanin abun da ya janyo tashin wutar ba.

“Sai dai abun takaici duk da kokarin namu mun kasa ceto yaran. Allah sa masu ceto ne.”

“Babu abun da aka cire a cikin gidan komai ya kone kurmus. Dabbobi ne kawai mutane suka iya cirosu ta saman garu, amma bayan tumakin gidan komai ya kone kurmus.”

Wakilinmu ya kuma shaida mana cewar, jami’an kashe gobara na jihar sun yi kokarin zuwa a kan lokaci wanda sun bada gagarumin gudunmawa wajen kashe wutar.

Sai dai lamarin ya tayar wa al’ummar unguwar hankali matuka.

Tuni aka yi jana’izar yaran kamar yadda addinin musulunci ya tanadar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Kuri’un CGTN: “Dimokaradiyyar Amurka” Ta Jefa Duniya Cikin Hargitsi

Kuri’un CGTN: “Dimokaradiyyar Amurka” Ta Jefa Duniya Cikin Hargitsi

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version