• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

by Sulaiman
1 month ago
AFSNET

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, zai yi jawabi a wani taro na habaka kasuwanci karo na biyar wanda AFSNET ke shiryawa.

 

Taron zai gudana daga ranar 4 zuwa 10 ga watan Satumba na shekarar 2025, a Cibiyar Habaka Kasuwanci (SAFEX) ta ƙasar Algeria.

  • Za Mu Kare Bukatun Nijeriya A Mashigin Tekun Guinea – Shettima
  • Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

Wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa an gayyaci Gwamna Lawal don yayi jawabi taron na AfSNET karo na biyar a ranar 6 ga watan Satumba na 2025.

 

LABARAI MASU NASABA

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

Sanarwar ta kuma ƙara da cewa, taron zai gudana ne a gefen bikin baje kolin kasuwanci tsakanin ƙasashen Afirka karo na huɗu (IATF2025).

 

“Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Aljeriya za ta ɗauki nauyin gudanar da bikin baje kolin kasuwanci tsakanin Afirka (IATF2025) sannan kuma bankin Afreximbank tare da haɗin gwiwar Hukumar Tarayyar Afirka (AUC) da Sakatariyar Yankin Kasuwancin Nahiyar Afirka (AfCFTA) za ta shirya shi.

 

“Bikin baje kolin kasuwanci tsakanin Afirka (IATF2025) zai samar da wani tsari na musamman kuma mai ƙima ga ‘yan kasuwa don samun kasuwa guda ɗaya ta Afirka ga sama da mutane biliyan 1.4 tare da habaka tattalin arzikin cikin gida na sama da dalar Amurka tiriliyan 3.5 da aka samar a ƙarƙashin yankin ciniki cikin ‘yanci na Nahiyar Afrika.

 

Taken taron na bana shi ne; ‘Ƙarfin Cikin Gida, Tasirin Duniya: Ƙarfafa gwamnatocin ƙasashen Afirka masu cikakken iko don samun ci gaba mai ɗorewa, yana nuna haɗin gwiwarmu don ba da damar gudanar da mulki na cikin gida don samun sakamako mai kyau na nahiyar.

 

“Sakamakon nasarar taron AfSNET karo na huɗu da aka gudanar a Kisumu na ƙasar Kenya, wanda ya tara gwamnoni sama da 45, magadan gari, shugabannin ƙananan hukumomi, masu zuba jari, da kuma abokan ci gaba daga ko’ina a nahiyar Afirka, taron na AfSNET ya jaddada muhimman dabaru na ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa wajen inganta kasuwanci cikin ‘yanci na nahiyar Afrika (AfCFTA).

 

“Taron ya gabatar da manyan tattaunawa, zaman zurfafa zuba jari, da hada-hadar B2B da B2G, wanda ya baiwa ‘yan ƙasashe damar gabatar da shirye-shiryen ci gaba da kuma gano hanyoyin samar da kuɗaɗe.

 

“Tare da mai da hankali sosai kan ci gaba da haɗin gwiwar yanki, taron na Kisumu ya kasance wani muhimmin dandali na tattara albarkatu da ƙarfafa haɗin gwiwa, da tsara hanyoyin da za a iya aiwatarwa da ajandar kasuwanci da ci gaban Afirka daga tushe.”

 

“An gayyaci Gwamna Lawal don yayi jawabi akan muhimmin abu cikin tattaunawar da za’ayi lura da ƙwarewar sa akan tattalin arziƙi da shugabanci.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja
Manyan Labarai

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya
Labarai

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

October 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

October 17, 2025
Next Post
Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

Ra’ayin Samar Da Ci Gaba Cikin Lumana: Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

LABARAI MASU NASABA

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
peter

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

October 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

October 17, 2025
Tinubu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
Shettima

‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 

October 17, 2025
Manzon Allah

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

October 17, 2025
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

October 17, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

October 17, 2025
Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.