• English
  • Business News
Wednesday, July 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

Ya Ƙaddamar Da Babban Asibitin Gusau Da Aka Gyara

by Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirinsa na sake farfaɗo da tsarin kiwon lafiya a Jihar Zamfara, tare da cika alƙawarin gwamnatinsa na samar da nagartacce kuma ingantaccen kiwon lafiya ga al’umma.

Gwamnan ya ƙaddamar da Babban Asibitin Gusau da aka gyara ciki-da-bai a ranar Juma’a.

  • Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal
  • Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa gyaran babban asibitin ya haɗa da sashin kula masu haɗurra da masu neman buƙatar kulawar gaggawa, sashen kwantar da mata masu juna biyu, ɗakunan haihuwa, sashin gudanarwar asibitin, ɗakin kula da yara, da kuma sashin kula da jarirai na musamman (SCBU).

Sauran sassan da aka gyara da kuma sanya kayan aiki sun haɗa da bangaren mata masu juna biyu tiyata, wurin zama jira, ɗakin kula da mata, babban ɗakin tiyata, sashen gwaje-gwaje na Radiology, sashen kula da ƙashi, sashen GOPD, da sashen kula da kunne, maƙogwaro, ido da harkar haƙori.

Zamfara

Labarai Masu Nasaba

Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati

Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai

A lokacin da yake jawabi a wurin ƙaddamarwar, Gwamna Lawal ya bayyana cewa da hawansa mulki a watan Mayun 2023, ya ci karo da tsarin kiwon lafiya da ya tabarbare saboda rashin kulawa.

Ya ce, “Gwamnatinmu, ƙarƙashin ginshiƙan shirye-shiryen ceto, nan da nan ta fara tantance abubuwan da asibitoci ke buƙata, inda sakamakon ya zama abin tsoro kuma ya nuna akwai jan-aiki.

“Alal misali, a jihar da ke da mutane kusan miliyan 6 tare da tarin ƙalubale, na’urar duban ɗan tayi ɗaya ce kawai a cikin dukkan cibiyoyin da gwamnati ta mallaka, kuma shi ma duk faci ne a jikinsa da salataf ko’ina! Nan take na ayyana dokar ta-baci a bangaren kiwon lafiya don dawo da ababen more rayuwa, samar da kayan aiki a asibitocinmu tare da samar da kwarin gwiwa da horarwa ga ƙwararru a fannin kiwon lafiya.

“Don inganta ayyukan more rayuwa, mun kuma ba da kwangilar samar da kayayyaki, sakawa, gwadawa, da horar da ma’aikata kan yadda za su yi amfani da na’urorin na zamani.

“Kamar yadda aka saba a wannan gwamnati ta Jihar Zamfara, muna tabbatar da cewa duk kayan aikin da aka kawo da kuma sanya su sun kasance masu inganci kuma sun cika ƙa’idojin da ake da su.

“Bari in jaddada cewa wannan ƙaddamarwar wani bangare ne na sake fasalin jihar Zamfara bakiɗaya a fannin kiwon lafiya, za ku iya tuna cewa mun riga mun samar da manyan asibitocin da aka gyara a garuruwan Ƙaura, Maradun, Maru, da Nasarawa Burkullu.

Zamfara

“Har ila yau, ana shirin ƙaddamar da wasu muhimman asibitocin da suka haɗa da Asibitin Ƙwararru na Ahmad Sani Yariman Bakura, Gusau, Babban Asibitin Talata Mafara, Shinkafi, da Babban Asibitin Tsafe, da dai sauransu.

“Bugu da ƙari, bayan amincewar majalisar zartarwa ta jiha, Ma’aikatar Lafiya ta fara aikin samar da cikakken kayan aiki ga manyan asibitocin da ke Anka, kuma wannan ya haɗa da samar da kayan aiki na zamani tare da horar da ma’aikatan kiwon lafiya.

“Ya ku ’yan uwa maza da mata, waɗannan ayyukan suna nuna hangen nesan mu na gina tsarin kiwon lafiya na zamani, mai aiki da kuma ɗorewa wanda zai rage yawan tura marasa lafiya zuwa wasu asibitoci a wajen jihar tare da tabbatar da cewa ’yan jihar mu sun sami ingantaccen kulawa kusa da gida.

“Yayin da muke murnar wannan nasarar, ina so in jawo hankalin mahukuntan asibitin kan buƙatar yin taka-tsan-tsan wajen amfani da kuma kula da wannan wuri.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Next Post

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

Related

Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati

47 minutes ago
Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai

2 hours ago
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci
Manyan Labarai

Har Yanzu Yaƙi Da Ta’addanci Ne Babban Muradin Gwamnatina — Tinubu

4 hours ago
Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa
Labarai

Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa

5 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Katsina, Sun Jikkata Mutane 2, Sun Sace Wasu

6 hours ago
Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa
Labarai

Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa

7 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Magance Yawan Soke Tashin Jirage Da Jinkiri A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Makarantun Kano Za Su Fara Hutun Ƙarshen Zango A Ranar Juma’a – Gwamnati

July 23, 2025
Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Taɓa Tauye ’Yancin Kafafen Yaɗa Labarai Ba, In ji Ministan Yaɗa Labarai

July 23, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Har Yanzu Yaƙi Da Ta’addanci Ne Babban Muradin Gwamnatina — Tinubu

July 23, 2025
Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa

Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa

July 23, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Katsina, Sun Jikkata Mutane 2, Sun Sace Wasu

July 23, 2025
Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa

Ɗan Shekaru 15 Ya Kashe Wani Matashi Kan Rikicin Gona A Jigawa

July 23, 2025
Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

Kwankwaso  Ne Kaɗai Ɗan Siyasar Da Zai Iya Maye Gurbin Buhari — Jigo A NNPP

July 22, 2025
Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

July 22, 2025
Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

July 22, 2025
Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

Taron Kolin Sin Da EU Zai Bayar Da Damar Zurfafa Hadin Gwiwar Sassan Biyu

July 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.