Gwamnatin jihar Kano ta ayyana ranar Litinin, 2 ga watan Yuni, 2025, a matsayin ranar hutu domin alhini da addu’o’i ga jaruman ‘yan wasan motsa jiki 22 da suka rasa rayukansu a wani mummunan hatsarin mota a yayin da suke dawowa daga gasar wasannin motsa jiki ta kasa a ranar Asabar.
Gwamna Abba Yusuf, a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, ya bayyana matukar bakin cikinsa kan wannan babban rashi, yana mai bayyana lamarin a matsayin “Bakar rana ga daukacin al’ummar jihar.”
- Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu
- Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo
LEADERSHIP ta ruwaito cewa, wadanda suka rasun na cikin tawagar jihar Kano a wani taron wasanni na kasa da aka kammala a birnin Abeokuta na jihar Ogun wanda ya hada ‘yan wasa daga sassan Nijeriya domin fafatawa a wasanni motsa jiki daban-daban.
Gwamna Yusuf wanda a halin yanzu yake kasar Saudiyya don gudanar da aikin hajjin 2025, ya bayar da umarnin ware ranar Litinin 2 ga watan Yunin 2025 a matsayin ranar hutu domin bai wa al’ummar damar yin jimami tare da yi wa wadanda suka rasu addu’a.
Ya kuma yi kira ga limamai da daukacin al’umma a fadin jihar, da su yi addu’o’i na musamman ga wadanda abin ya shafa da kuma karfafa wa iyalansu da suka rasu.
Gwamna Yusuf ya tabbatar da cewa, gwamnati na daukar matakan tallafawa wadanda suka jikkata da kuma iyalan wadanda abin ya shafa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp