• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan CBN Ya Gargadi Nijeriya Kan Hatsarin Laftan Basuka

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan CBN Ya Gargadi Nijeriya Kan Hatsarin Laftan Basuka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Olayemi Cardoso, ya gargadi Nijeriya da sauran kasashe masu tasowa da su yi taka-tsan-tsan kan hadarin bashi, yana mai cewa idan ba a magance su ba za su kawo cikas ga ci gaba n tattalin arziki da wadata.

Gwamnan CBN ya kuma ce a halin da Nijeriya ke ciki na gaf da shiga hatsarin basuka, duba da halin da kasuwan duniya ke ciki da kuma karuwar basuka da ya samu asali tun daga barkewar cutar Korona.

  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Abinci A Jihohi
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kara Gina Madatsun Ruwa Domin Noman Rani

Masana da dama dai sun jima suna yekuwar cewa tulin basukan da Nijeriya ke kai ne suka zama asasin matsalolin tattalin arziki da ke kara haifar da matsaloli a kasar nan musamman na matsin rayuwa.

Duk da basuka masu yawa da ake bin Nijeriya na ciki da waje, har yanzu jagororin kasar a matakin tarayya da jihohi na ci gaba da kinkimo wa kansu basuka.

Lamarin da ke kara maida al’umman kasar cikin mummunn talauci da fatara, musamman tun bayan cire tallafin man fetur a farkon hawan wannan gwamnatin da kuma karyewar darajar naira.

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

Sai dai Cardoso ya ce, hatsarin da babban bankin duniya da asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) suka bayyana, na nuni da cewa Nijeriya na fuskantar barazana.

Ya shaida hakan ne a Abuja lokacin kaddamar da taron masu ruwa da tsaki kan basuka na bankin duniya, IMF, (WAIFEM).

Ya samu wakilcin daraktan tsare-tsaren kudade, Dakta Mohammed Musa Tumala, ya ce, “Domin tabbatar da harkokin ciyo basuka na gudana bisa matakin da suka dace, kauce wa fadawa cikin hatsari da kuma shawo kansu.”

Ya ce, dole ne ya zama duk wani bashin da za a ciyo a yi nazari kuma a tabbatar an bi matakan ciyo bashi domin tabbatar da kiyaye matsalolin da ka iya janyowa a nan gaba.

Ana bin jihohi da gwamnatin tarayya basukan da suka kai naira tiriliyan 139, a rahotonnin da suke akwai.

A jawabinsa tun da farko, daraktan cibiyar hada-hadar kudade da tattalin arziki na Yammacin Afrika, (WAIFEM), Dakt Baba Y. Musa, ya shawarci gwamnatin tarayya da ta maida hankali kan barazanar kara tara wa kanta basuka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikita-rikitar Sauka Da Komawar Sheikh Daurawa Shugabancin Hisbar Jihar Kano

Next Post

Ba Za Mu Lamunci Cin Zarafin Wani Da Sunan Tafsiri Ba – Gwamnatin Kaduna

Related

Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21
Labarai

Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21

19 minutes ago
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano
Labarai

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

1 hour ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

2 hours ago
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

3 hours ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

3 hours ago
Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota
Manyan Labarai

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

3 hours ago
Next Post
Uba sani

Ba Za Mu Lamunci Cin Zarafin Wani Da Sunan Tafsiri Ba - Gwamnatin Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

May 31, 2025
Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21

Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21

May 31, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

May 31, 2025
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

May 31, 2025
Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

May 31, 2025
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

May 31, 2025
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

May 31, 2025
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

May 31, 2025
Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota

May 31, 2025
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.