• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan CBN Ya Gargadi Nijeriya Kan Hatsarin Laftan Basuka

by Khalid Idris Doya
2 years ago
CBN

Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Olayemi Cardoso, ya gargadi Nijeriya da sauran kasashe masu tasowa da su yi taka-tsan-tsan kan hadarin bashi, yana mai cewa idan ba a magance su ba za su kawo cikas ga ci gaba n tattalin arziki da wadata.

Gwamnan CBN ya kuma ce a halin da Nijeriya ke ciki na gaf da shiga hatsarin basuka, duba da halin da kasuwan duniya ke ciki da kuma karuwar basuka da ya samu asali tun daga barkewar cutar Korona.

  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Abinci A Jihohi
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kara Gina Madatsun Ruwa Domin Noman Rani

Masana da dama dai sun jima suna yekuwar cewa tulin basukan da Nijeriya ke kai ne suka zama asasin matsalolin tattalin arziki da ke kara haifar da matsaloli a kasar nan musamman na matsin rayuwa.

Duk da basuka masu yawa da ake bin Nijeriya na ciki da waje, har yanzu jagororin kasar a matakin tarayya da jihohi na ci gaba da kinkimo wa kansu basuka.

Lamarin da ke kara maida al’umman kasar cikin mummunn talauci da fatara, musamman tun bayan cire tallafin man fetur a farkon hawan wannan gwamnatin da kuma karyewar darajar naira.

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Sai dai Cardoso ya ce, hatsarin da babban bankin duniya da asusun bayar da lamuni na duniya (IMF) suka bayyana, na nuni da cewa Nijeriya na fuskantar barazana.

Ya shaida hakan ne a Abuja lokacin kaddamar da taron masu ruwa da tsaki kan basuka na bankin duniya, IMF, (WAIFEM).

Ya samu wakilcin daraktan tsare-tsaren kudade, Dakta Mohammed Musa Tumala, ya ce, “Domin tabbatar da harkokin ciyo basuka na gudana bisa matakin da suka dace, kauce wa fadawa cikin hatsari da kuma shawo kansu.”

Ya ce, dole ne ya zama duk wani bashin da za a ciyo a yi nazari kuma a tabbatar an bi matakan ciyo bashi domin tabbatar da kiyaye matsalolin da ka iya janyowa a nan gaba.

Ana bin jihohi da gwamnatin tarayya basukan da suka kai naira tiriliyan 139, a rahotonnin da suke akwai.

A jawabinsa tun da farko, daraktan cibiyar hada-hadar kudade da tattalin arziki na Yammacin Afrika, (WAIFEM), Dakt Baba Y. Musa, ya shawarci gwamnatin tarayya da ta maida hankali kan barazanar kara tara wa kanta basuka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Majalisar Dattawa
Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Next Post
Uba sani

Ba Za Mu Lamunci Cin Zarafin Wani Da Sunan Tafsiri Ba - Gwamnatin Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.