• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Bayar Da Umurnin Raba Kayan Abinci Don Rage Raɗaɗin Kuncin Rayuwa

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Gombe Ya Bayar Da Umurnin Raba Kayan Abinci Don Rage Raɗaɗin Kuncin Rayuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani mataki na daƙile ƙalubalen tattalin arziƙin da al’ummar Jihar Gombe ke fuskanta a halin yanzu, Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya amince da raba kayan abinci ga marassa galihu a faɗin jihar.

 

Hakan na zuwa ne bayan ƙudurin hakan da aka cimma a babban taron majalisar tsaron jihar da Gwamna Inuwa Yahaya ya jagoranta ranar Litinin kan matsalolin da zanga-zangar matsin rayuwa ya janyo a jihar.

  • ‘Yansanda Sun Ja Hankalin Jama’a Kan Su Guji Rikiɗewar Zanga-zanga Zuwa Rikici A Ribas 
  • Gwamnatin Filato Ta Sassauta Dokar Hana Fita A Jihar

Don haka Gwamnan ya amince da raba buhunan dawa dubu masu nauyin kilogiram 50-50 da buhunan shinkafa dubu masu nauyin kilogiram 25 da katon dubu na taliya ga kowace ƙaramar hukuma cikin ƙananan hukumomi 11 na Jihar Gombe.

 

Labarai Masu Nasaba

Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

Hakazalika, za a raba irin wannan tallafin abinci, buhuna 5,000 da katon-katon na taliya ga ƙungiyoyin addini, da ƙungiyoyin fararen hula, da ƙungiyoyin ɗalibai (GOSSA da NANS), da makarantun tsangaya da almajirai, da ƙungiyoyin matasa da mata da kuma masu buƙata ta musamman da sauran jama’a masu rauni a cikin al’umma.

 

Da ya ke karin haske kan wannan lamarin, kakakin gwamnan Malam Ismaila Uba Misilli ya ce wannan dai shi ne karo na 19 da gwamnatin jihar za ta raba irin wannan tallafi ga al’ummar Jihar Gombe a ci gaba da ƙoƙarin samar da agaji da inganta rayuwar al’ummar jihar a wannan mawuyacin lokaci.

 

“Ana sa ran tallafin abincin zai taimaka matuƙa wajen rage wahalhalun da jama’a da dama ke fama da su a jihar, musamman ma masu rauni.”

 

Ya kara da cewa, “Gwamna Inuwa Yahaya, ya ƙara jajircewa wajen aiwatar da ingantattun matakan tallafawa jama’a don sauƙaƙa musu rayuwa a tsaka da fama da ƙalubalen tattalin arziƙin da ake ciki.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCGwamnatin TinubuTabarbarewar Tattalin ArzikiTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Na Kan Gaba Wajen Neman Ikon Mallakar Fasaha A Fannin Kiyaye Muhalli A Duniya 

Next Post

Cinikayya Tsakanin Sin Da Kasashen Ketare Ya Karu Da Kaso 6.2 A Watanni 7 Na Farkon Bana

Related

Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet
Labarai

Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

33 minutes ago
An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato
Labarai

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

3 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

5 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

8 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

9 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

17 hours ago
Next Post
Cinikayya Tsakanin Sin Da Kasashen Ketare Ya Karu Da Kaso 6.2 A Watanni 7 Na Farkon Bana

Cinikayya Tsakanin Sin Da Kasashen Ketare Ya Karu Da Kaso 6.2 A Watanni 7 Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

August 22, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

August 22, 2025
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

August 22, 2025
Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

August 22, 2025
An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.