• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Bayar Da Umurnin Raba Kayan Abinci Don Rage Raɗaɗin Kuncin Rayuwa

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Gombe Ya Bayar Da Umurnin Raba Kayan Abinci Don Rage Raɗaɗin Kuncin Rayuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani mataki na daƙile ƙalubalen tattalin arziƙin da al’ummar Jihar Gombe ke fuskanta a halin yanzu, Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ya amince da raba kayan abinci ga marassa galihu a faɗin jihar.

 

Hakan na zuwa ne bayan ƙudurin hakan da aka cimma a babban taron majalisar tsaron jihar da Gwamna Inuwa Yahaya ya jagoranta ranar Litinin kan matsalolin da zanga-zangar matsin rayuwa ya janyo a jihar.

  • ‘Yansanda Sun Ja Hankalin Jama’a Kan Su Guji Rikiɗewar Zanga-zanga Zuwa Rikici A Ribas 
  • Gwamnatin Filato Ta Sassauta Dokar Hana Fita A Jihar

Don haka Gwamnan ya amince da raba buhunan dawa dubu masu nauyin kilogiram 50-50 da buhunan shinkafa dubu masu nauyin kilogiram 25 da katon dubu na taliya ga kowace ƙaramar hukuma cikin ƙananan hukumomi 11 na Jihar Gombe.

 

Labarai Masu Nasaba

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Hakazalika, za a raba irin wannan tallafin abinci, buhuna 5,000 da katon-katon na taliya ga ƙungiyoyin addini, da ƙungiyoyin fararen hula, da ƙungiyoyin ɗalibai (GOSSA da NANS), da makarantun tsangaya da almajirai, da ƙungiyoyin matasa da mata da kuma masu buƙata ta musamman da sauran jama’a masu rauni a cikin al’umma.

 

Da ya ke karin haske kan wannan lamarin, kakakin gwamnan Malam Ismaila Uba Misilli ya ce wannan dai shi ne karo na 19 da gwamnatin jihar za ta raba irin wannan tallafi ga al’ummar Jihar Gombe a ci gaba da ƙoƙarin samar da agaji da inganta rayuwar al’ummar jihar a wannan mawuyacin lokaci.

 

“Ana sa ran tallafin abincin zai taimaka matuƙa wajen rage wahalhalun da jama’a da dama ke fama da su a jihar, musamman ma masu rauni.”

 

Ya kara da cewa, “Gwamna Inuwa Yahaya, ya ƙara jajircewa wajen aiwatar da ingantattun matakan tallafawa jama’a don sauƙaƙa musu rayuwa a tsaka da fama da ƙalubalen tattalin arziƙin da ake ciki.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCGwamnatin TinubuTabarbarewar Tattalin ArzikiTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Na Kan Gaba Wajen Neman Ikon Mallakar Fasaha A Fannin Kiyaye Muhalli A Duniya 

Next Post

Cinikayya Tsakanin Sin Da Kasashen Ketare Ya Karu Da Kaso 6.2 A Watanni 7 Na Farkon Bana

Related

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana
Labarai

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

5 hours ago
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
Labarai

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

6 hours ago
Shettima
Labarai

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

7 hours ago
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 
Labarai

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

8 hours ago
Boko Haram Na Yin TikTok, Suna Sarrafa Jirage Marasa Matuƙi Don Sa Ido Kan Sansanonin Soji – Bulama 
Labarai

Ƙwararren Masanin Tsaro, Bulama Ya Ƙaryata Iƙirarin El-Rufai Kan Biyan ’Yan Bindiga Kuɗaɗen Fansa

10 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

11 hours ago
Next Post
Cinikayya Tsakanin Sin Da Kasashen Ketare Ya Karu Da Kaso 6.2 A Watanni 7 Na Farkon Bana

Cinikayya Tsakanin Sin Da Kasashen Ketare Ya Karu Da Kaso 6.2 A Watanni 7 Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.