• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Jaddada Kudurin Tallafa Wa Matasa Ta Hanyar Fasahar Zamani

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya jaddada kudurinsa na fadada harkokin gwamnatinsa na fasahar zamani don tabbatar da cewa ilimin zamani ya samu cikin sauki a yunkurinsa na samar da kyakkyawar makoma ga matasan Jihar Gombe a duniyar yau mai saurin ci gaba.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a sakonsa ga al’ummar jihar, yayin da ake alamta bikin ranar matasa ta duniya ta bana a wata sanarwar mai dauke da sanya hannun kakakinsa Isra’ila Uba Misilli.

  • Kudaden ‘Yan Majalisa: Wa Za A Gaskata Tsakanin Hukumar Albashi Da Kawu Sumaila?
  • Super Falons Ta Cigaba Da Zama Ta 36 A Jadawalin Iya Taka Leda Na FIFA

Ya ce taken ranar ta bana, “Daga Latsawa Zuwa Ci Gaba: Dabarun Zamani Ga Matasa Don Ci Gaba Mai Dorewa,” ya yi daidai da kudurin gwamnatinsa na tallafawa matasa ta hanyar Kirkire-kirkiren zamani.

 

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Gwamna Inuwa Yahaya ya jaddada cewa gwamnatinsa tana ci gaba da maida hankali a fannin ilimi, da koyar da sana’o’i, da kasuwanci, da samar da ayyukan yi, tare da bunkasa wadata ga matasa da samar musu kayan aikin da suke buata don damawa da su a duniyar zamani. Ya kara da cewa, wadannan yunkuri suna da muhimmanci ga hangen nesan samar da makoma mai dorewa ga matasan jihar dana kasa baki daya.

 

Gwamna Inuwa Yahaya, ya ce gwamnatinsa ta kaddamar da wassu shirye-shiryen zamani don bai wa matasa sana’o’in hannu da nufin bunkasa fasaharsu a duniyar zamani. Daya daga cikin wadannan manyan shirye-shiryen shine na yin ayyuka ga kamfanonin kasashen waje daga nan gida Nijeriya wato Outsource to Nigeria Initiatibe (OTNI), inda aka ba da gudummawar cibiyar koyon sana’o’i da kudade don hadaka fasahar sadarwa don tallafawa matasa 2,000 da aka horar kan fasahar zamani da samar musu ayyukan yi.

 

Ya yaba da jajircewa da kirkire-kirkiren da matasa suke yi wajen kawo sauyi mai ma’ana a cikin al’umma, inda ya jaddada muhimmiyar rawar da fasahar zamani ke takawa wajen kyautatawar gobe, ya kuma bukaci matasan su rungumi damammakin fasahar zamani don sarrafa iliminsu wajen bada tasu gudunmawa ga jihar da samar da ci gaba mai dorewa.

 

“Matasanmu ba shugabannin gobe ba ne kawai, su ne ma masu kawo canji a yau, idan suka samu kayan aiki da damammakin da suka dace, za su iya cimma dimbin nasarori. Tare za mu gina Jihar Gombe inda kowane matashi zai iya sarrafa fasahar zamani zuwa ci gaba, da kuma burukanmu baki daya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Harba Gungun Taurarin Dan Adam Na Binciken Doron Kasa

Next Post

Adadin Kunshin Kaya Da Aka Yi Jigila Cikin Sauri A Sin Ya Karu Da Kaso 22.2% A Yuli

Related

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

2 weeks ago
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

5 months ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

6 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

7 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

7 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

12 months ago
Next Post
Adadin Kunshin Kaya Da Aka Yi Jigila Cikin Sauri A Sin Ya Karu Da Kaso 22.2% A Yuli

Adadin Kunshin Kaya Da Aka Yi Jigila Cikin Sauri A Sin Ya Karu Da Kaso 22.2% A Yuli

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.