• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Jaddada Kudurin Tallafa Wa Matasa Ta Hanyar Fasahar Zamani

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya jaddada kudurinsa na fadada harkokin gwamnatinsa na fasahar zamani don tabbatar da cewa ilimin zamani ya samu cikin sauki a yunkurinsa na samar da kyakkyawar makoma ga matasan Jihar Gombe a duniyar yau mai saurin ci gaba.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a sakonsa ga al’ummar jihar, yayin da ake alamta bikin ranar matasa ta duniya ta bana a wata sanarwar mai dauke da sanya hannun kakakinsa Isra’ila Uba Misilli.

  • Kudaden ‘Yan Majalisa: Wa Za A Gaskata Tsakanin Hukumar Albashi Da Kawu Sumaila?
  • Super Falons Ta Cigaba Da Zama Ta 36 A Jadawalin Iya Taka Leda Na FIFA

Ya ce taken ranar ta bana, “Daga Latsawa Zuwa Ci Gaba: Dabarun Zamani Ga Matasa Don Ci Gaba Mai Dorewa,” ya yi daidai da kudurin gwamnatinsa na tallafawa matasa ta hanyar Kirkire-kirkiren zamani.

 

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Gwamna Inuwa Yahaya ya jaddada cewa gwamnatinsa tana ci gaba da maida hankali a fannin ilimi, da koyar da sana’o’i, da kasuwanci, da samar da ayyukan yi, tare da bunkasa wadata ga matasa da samar musu kayan aikin da suke buata don damawa da su a duniyar zamani. Ya kara da cewa, wadannan yunkuri suna da muhimmanci ga hangen nesan samar da makoma mai dorewa ga matasan jihar dana kasa baki daya.

 

Gwamna Inuwa Yahaya, ya ce gwamnatinsa ta kaddamar da wassu shirye-shiryen zamani don bai wa matasa sana’o’in hannu da nufin bunkasa fasaharsu a duniyar zamani. Daya daga cikin wadannan manyan shirye-shiryen shine na yin ayyuka ga kamfanonin kasashen waje daga nan gida Nijeriya wato Outsource to Nigeria Initiatibe (OTNI), inda aka ba da gudummawar cibiyar koyon sana’o’i da kudade don hadaka fasahar sadarwa don tallafawa matasa 2,000 da aka horar kan fasahar zamani da samar musu ayyukan yi.

 

Ya yaba da jajircewa da kirkire-kirkiren da matasa suke yi wajen kawo sauyi mai ma’ana a cikin al’umma, inda ya jaddada muhimmiyar rawar da fasahar zamani ke takawa wajen kyautatawar gobe, ya kuma bukaci matasan su rungumi damammakin fasahar zamani don sarrafa iliminsu wajen bada tasu gudunmawa ga jihar da samar da ci gaba mai dorewa.

 

“Matasanmu ba shugabannin gobe ba ne kawai, su ne ma masu kawo canji a yau, idan suka samu kayan aiki da damammakin da suka dace, za su iya cimma dimbin nasarori. Tare za mu gina Jihar Gombe inda kowane matashi zai iya sarrafa fasahar zamani zuwa ci gaba, da kuma burukanmu baki daya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Harba Gungun Taurarin Dan Adam Na Binciken Doron Kasa

Next Post

Adadin Kunshin Kaya Da Aka Yi Jigila Cikin Sauri A Sin Ya Karu Da Kaso 22.2% A Yuli

Related

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

2 weeks ago
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

5 months ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

6 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

7 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

7 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

12 months ago
Next Post
Adadin Kunshin Kaya Da Aka Yi Jigila Cikin Sauri A Sin Ya Karu Da Kaso 22.2% A Yuli

Adadin Kunshin Kaya Da Aka Yi Jigila Cikin Sauri A Sin Ya Karu Da Kaso 22.2% A Yuli

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.