• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Sake Biyan Biliyan 5.4 Na Giratuti, Ya Rage Bashin Giratutin Da Ya Gada Daga Biliyan 21 Zuwa Biliyan 7

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Gombe Ya Sake Biyan Biliyan 5.4 Na Giratuti, Ya Rage Bashin Giratutin Da Ya Gada Daga Biliyan 21 Zuwa Biliyan 7
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ƙaddamar da wani sabon rukuni na biyan kuɗaɗen sallama ga tsofin ma’aikatan jihar da na ƙananan hukumomi su fiye da mutum 4,000 da suka yi ritaya daga aiki tare da yin alkawarin biyan sauran haƙƙoƙin ma’aikatan da suka yi ritayan. 

A wannan karon, gwamnatin jihar za ta biya kuɗaɗen sallaman da suka kai Naira biliyan 5 da miliyan 440 da dubu 45 da 865 da Kobo 73 ga tsofin ma’aikatan na jiha da ƙananan hukumomi.

  • Ramadan: Maryam Abacha Ta Nemi Attajirai Su Tallafa Wa Mabukata
  • An Kammala Canja Fasalin Gasar Cin Kofin Zakarun Turai

Hakan dai yana nufin an rage basussukan da tsofin ma’aikatan ke bin gwamnati daga naira biliyan 21 zuwa Naira biliyan 7, kamar yadda Ismaila Uba Misilli ya tabbatar a sanarwar da ya aiko mana.

Da ya ke jawabi yayin bikin da aka gudanar a gidan gwamnati, Gwamna Inuwa Yahaya ya jaddada ƙudurin gwamnatinsa na inganta jin dadin ma’aikata dama waɗanda suka yi ritaya, yana mai yaba wa irin gudunmawar da suke bayarwa ga ci gaban Jihar Gombe.

Gwamnan ya tuno cewa bayan hawansa mulki a 2019, ɗaya daga cikin manyan ƙalubalen da gwamnatinsa ta gada shi ne na bashin fiye da naira biliyan 21 na kuɗaɗen giratuti da waɗanda suka yi ritaya suke bin gwamnatin jihar da ƙananan hukumomi.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Ya ci gaba da cewa, a ƙoƙarinta na tabbatar da gaskiya da adalci, gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancinsa ta ba da fifiko wajen magance matsalar baki ɗaya, don haka cikin shekaru biyar da suka gabata ta biya fiye da Naira biliyan 7 na bashin kuɗaɗen giratutin da ta gada.

Ya ce, “A wannan zagayen, za mu biya kuɗaɗen da suka kai naira biliyan 5 da miliyan 440 da dubu 45 da 865 da Kobo 73 ga wasuka yi ritaya daga jiha da ƙananan hukumomi. Gwamnatin jihar za ta biya giratuti na shekarar 2018, ƙananan hukumomi kuma za su biya ne gwargwadon ƙarfin aljihun kowace ƙaramar hukuma, inda ƙananan hukumomi masu karfin tattalin arziƙi za su iya biyan fiye dana takwarorinsu masu ƙaramin ƙarfi,” in ji Gwamnan.

Ya ƙara da cewa, “Don haka ƙananan hukumomin Kwami, da Funakaye da Nafaɗa za su iya biyan duk bashin giratutin da ake binsu; Akko da Ɓillliri, da Dukku da Shongom za su biya giratuti na 2014 da 2015, Balanga da Yamaltu Deba kuma za su biya na 2013 da 2014, yayin da Kaltungo da Gombe za su biya waɗanda suka yi ritaya na 2013 ne kawai. Wannan tsarin zai taimaka sosai wajen ƙarfafa gaskiya da riƙon amana, don ya dace da kowace ƙaramar hukuma.

Gwamna Inuwa Yahaya ya yi ƙira ga ma’aikatan jihar su ruɓanya ƙoƙari tare da nuna jajircewarsu wajen gudanar da ayyuka, inda ya bayyana kwazo da jajircewarsu masu a matsayin ɗaya daga cikin nasarorin gwamnati mai ci.

Gwamnan ya yi gargaɗin cewa “Gwamnatinmu ba za ta lamunci duk wani nau’i na rashin ɗa’a ko rashin gaskiya da zai iya ɓata sunan ma’aikatan gwamnati dama na Jihar Gombe baki ɗaya ba, muna sa ran kowane ma’aikacin gwamnati ya nuna kyakkyawan misali na gaskiya, ƙwarewa da kuma riƙon amana a halaye da mu’amalarsa”.

Gwamnan ya yabawa shugabannin kwadago, da shugabannin ƙungiyoyin ma’aikatan da suka yi ritaya, da sauran masu ruwa da tsaki bisa haƙuri, fahimta, haɗin kai da kuma jajircewarsu wajen tattaunawa a lokacin da ake kokarin magance koma-baya da aiwatar da gyare-gyare a harkar aikin gwamnati.

Tun farko a jawabinsa na maraba, babban mai binciken kuɗi na jiha kuma shugaban kwamitin biyan giratutin Muhammad Buba Gombe, ya amince da ƙoƙarin da gwamnan ya yi wajen magance matsalar rashin biyan giratuti tun hawansa mulki a 2019.

Ya ƙara da cewa sakamakon wannan amincewar na baya-bayan nan, jimillar kuɗaɗen gratutin da gwamnatin ta biya sun kai Naira biliyan 12, miliyan 736 da dubu 228 da 885. Ya zuwa yanzu mai girma gwamna ya amince da biyan kudin giratuti na tsofin ma’aikatan jiha dana ƙananan hukumomi”.

Da yake jawabi a madadin ɗokacin waɗanda za su ci gajiya, Garba Sama’ila, ya godewa Gwamna Inuwa da ya kawo musu ɗauki a wannan mawuyacin lokaci na taɓarɓarewar tattalin arziƙi.

Yace da wannan karimcin, Gwamnan ba kawai biyan giratuti ga ma’aikatan da suka yi ritaya ya yi ba, har ma da ceto ga miliyoyin iyalansu daga mummunar matsalar tattalin arzikin da ake ciki a yau.

Malam Garba ya kuma yi alkawarin cewa duk waɗanda suka yi ritayan za su mara baya ga tsare-tsare da manufofin gwamnatin Inuwa, inda ya bayyana Gwamnan a matsayin “shugaba mai jin ƙai kuma aminin waɗanda suka yi ritaya”.

Muhimman ababen da suka fi ɗaukar hankali a taron su ne gabatar da cekin kuɗi ga waɗanda suka yi ritayar, waɗanda galibinsu suka bar aikin tun a shekarar 2013 amma ba su sami hakkokinsu ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gombe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ramadan: Maryam Abacha Ta Nemi Attajirai Su Tallafa Wa Mabukata

Next Post

Masani Dan Najeriya Na Dora Muhimmanci Kan Raya Sabon Karfin Samar Da Hajoji Da Hidimomi Masu Karko Da Sin Ke Yi

Related

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

39 minutes ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

4 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

6 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

9 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

10 hours ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

13 hours ago
Next Post
Sin

Masani Dan Najeriya Na Dora Muhimmanci Kan Raya Sabon Karfin Samar Da Hajoji Da Hidimomi Masu Karko Da Sin Ke Yi

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.