Gwamnan jihar Kano, Abba Yusuf Kabir ya isa kasar Amurka domin wani gagarumin taron tattaunawa da Cibiyar Zaman Lafiya ta Amurka ta shirya.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban sakataren yada labarai na gwamnan, Sunusi Bature ya fitar a ranar Laraba.
- Zan Yi Murabus Matukar Ba A Gurfanar Da Yahaya Bello Ba – Shugaban EFCC
- EFCC Ta Sake Maka Emefiele A Kotu Kan Wasu Sabbin Tuhume-tuhume 4
Taron wanda za a shafe kwanaki uku ana gudanarwa, ya samu halartar gwamnonin Kano, Katsina, Zamfara, Kaduna, Neja, Sokoto, Kebbi, Jigawa, da Filato.
Bature ya ce, taron ana sa ran zai kawo hanyoyin da za a bi don magance matsalar rashin tsaro a Arewacin Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp