• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kano Ya Taya Sanata Kwankwaso Murnar Cika Shekaru 67

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Kwankwaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano, ya taya tsohon Gwamnan Kano, jagoran Kwankwasiyya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na NNPP a zaɓen 2023, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, murnar cika shekaru 67 a duniya.

Cikin wata sanarwar mai taken: Taya madugu Uban Tafiya murnar cika shekaru 67 da haihuwa, wacce mai magana da yawun gwamnan jihar, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a safiyar Asabar, 21 ga Oktoba, Gwamna Abba ya jinjina wa Kwankwaso bisa kishin al’umma, jagoranci nagari da aiki tuƙuru da ya yi fice a kai.

  • Saboda Kishin Ilimi Muka Raba Wa Makarantun Kano Littafai Sama Da Miliyan 2 – Kwamishinan Addini
  • Babbar Matsalar Nijeriya, Rashin Shugabanci Nagari – Wike

“A madadin al’ummar Jihar Kano, mai Girma Gwamna, Injiniya Abba Kabir Yusuf na cike da farin cikin taya shugabanmu, madugunmu kuma hasken fitilarmu –  Mai Girma Sanata Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso PhD, FNSE, murnar cika shekaru 67 masu albarka a duniya.”

Abba ya jaddada cewa, Kwankwaso mutum ne nagari, mai aƙida ta ƙwarai, juriya da hangen nesa.

“Kyakkyawar aƙidarka ta gina al’umma, babban misali ne abin koyi ga dukkan shugabannin wannan zamani.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

“Nasarorin da ka cimma da ayyukan da ka aiwatar sun tabbatar da kyakkyawar aƙidarka ta kishin al’umma da tsayin-daka kan nagartacciyar turbar siyasa, domin sadaukar da kai ga jiharmu da ƙasa a kowane lokaci.”

Daga nan sai gwamnan ya yi addu’a Allah ya ƙara wa Kwankwaso lafiya da ƙarfin hali da hikimar ci gaba da yi musu jagoranci, har ya dangana ga ƙololuwar nasara nan ba da daɗewa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abba Gida-gidakanoKwankwaso
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Sashen Fasaha Na Nijeriya Ya Yi Fintikau Wajen Samun Zuba Jari

Next Post

‘Yansanda Na Bincike Kan Musabbabin Mutuwar Kwamishinan ‘Yan Gudun Hijira Na Jihar Borno

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

5 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

5 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

15 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

17 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

18 hours ago
Next Post
‘Yansanda Na Bincike Kan Musabbabin Mutuwar Kwamishinan ‘Yan Gudun Hijira Na Jihar Borno

'Yansanda Na Bincike Kan Musabbabin Mutuwar Kwamishinan 'Yan Gudun Hijira Na Jihar Borno

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.