• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Katsina Ya Nuna Takaicinsa Kan ‘Yan Kasuwar Da Ke Boye Abinci 

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Katsina Ya Nuna Takaicinsa Kan ‘Yan Kasuwar Da Ke Boye Abinci 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Katsina Dikko Umaru Radda, ya nuna matukar takaicinsa kan yadda wasu ‘yan kasuwa a jihar ke boye kayan masarufi, musamman shinkafa sakamakon rufe iyakokin wannan kasa.

Radda, ya bayyana hakan ne a cikin wata sanawa da Kakakinsa Ibrahim Kaula Mohammed ya fitar a jihar, inda gwamnan ya yi nuni da cewa wannan dabi’a ta ‘yan kasuwa ba karamar abar kaico ba ce, musamman ganin yadda gwamnati ke nuna damuwarta kan yadda kayan masarufi ke ci gaba da yin tashin gwaron zabi a jihar.

  • SEMA Ta Raba Kayayyakin Gini Na Miliyan N50 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Jihar Katsina

Ya kara da cewa, sakamakon tashin farashin kayan masarufi a jihar ne ya sanya, kwanakin baya gwamnatin jihar ta amince da fitar da hatsi da takin zamani kimanin buhu dubu 39, 100, don raba wa masu karamin karfi da sauran manoma kyauta, don rage musu radadin kuncin halin rayuwar da suke ciki.

A cewar tasa, Gwamnatin Jihar ta lura wasu daga cikin ‘yan kasuwar jihar na boye kayan masarufi, domin haifar da karancin a fadin su a jihar, wanda hakan kan jawo tashin farashin nasu.

“A kwannan baya gwamnatin jihar ta amince da fitar da hatsi da takin zamani, don raba wa marasa karfi da manoma, musamman kanana da ke fadin jihar akalla buhunhunan hatsi dubu 39,100 kyauta, don rage musu radadin kuncin rayuwa”, in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Radda ya ci gaba da cewa, gwamnatinsa ko kadan ba za ta lamunta tare da saurara wa ire-iren wadannan ‘yan kasuwa marasa kishi da tausayin talakawa ba, za kuma su ci gaba da sanya idanu a kansu domin dakile ci gaba da afkuwar hakan.

“Mun lura wasu ‘yan kasuwa a jihar na boye kayan masarufi domin haifar da karancin abinci a wannan jiha, wanda hakan zai matukar jawo tashin farashinsu matuka gaya.”

A karshe, gwamnan ya bukaci al’ummar jihar da su mayar da hankali wajen sanar da mahukunta a fadin jihar sahihan bayanai a kan ire-iren wadannan ‘yan kasauwa marasa kishi da ke yi wa Gwamnatin Jihar zagon kasa na yunkurinta na samar da abinci a kan farashi mai sauki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojojin Nijar Za Su Mika Mulki Nan Da Shekara 3 – Janar Tchiani

Next Post

Lai Ching-te Dan Tada Hargitsi Ne

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

1 hour ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

4 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

5 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

14 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

16 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

17 hours ago
Next Post
Lai Ching-te Dan Tada Hargitsi Ne

Lai Ching-te Dan Tada Hargitsi Ne

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.