• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kebbi Ya Kaddamar Da Aikin Titi A Garin Argungu Kan Kudi Fiye Da Naira Biliyan 7.2 

by Umar Faruk and Sulaiman
1 year ago
Kebbi

Gwamnan jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris ya kaddamar da aikin gina titi a Garin Argungu wanda zai lakume kusan Naira biliyan 7.23

 

Kamfanin Amirco Universal Concept LTD ne zai yi kwangilar wacce ake sa ran kammala ta cikin watanni 12 masu zuwa.

  • Babu Shirin Rushe Babban Masallacin Jalingo – Gwamnatin Taraba
  • Ban Ji Dadin Abin Da Libya Ta Yi Wa Super Eagles Ba – Tinubu

Jimlar tsarin gudanar da aikin shine kamar haka: Tagwayen Hanyoyi na Tsohon Bye-Pass aka Naira Miliyan 6.83; Mayar da Bututun Samar da ruwan Sha da aka binne a kasa kafin shimfida Titin, akan Naira miliyan 63.92; Biyan diyyar Gidajen da aikin titin ya biyo ta kansu akan Naira Miliyan 339.91

 

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

Kwamishinan Ayyuka, Hon. Abdullahi Umar Faruk Muslim, ya yabawa Gwamna Idris bisa yadda ya mika aikin ga fitaccen kamfani don tabbatar da cewa, an gudanar da aiki mai inganci.

 

A nasa jawabin, Mai martaba Sarkin Kabin Argungu, Alhaji Samaila Muhammad Mere, ya nuna jin dadinsa ga Gwamnan bisa cika alkawuran da ya dauka a yakin neman zabensa na gina tituna a dukkan masarautu hudu da ke jihar Kebbi.

 

Gwamna Idris ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta cika kashi 60 cikin 100 na alkawurran da ta yi wa masarautar Argungu dangane da samar da ayyukan more rayuwa. Ya kuma bayyana shirin bayar da kwangilar gyaran babban asibitin Argungu, bisa la’akari da halin da ya ke ciki a halin yanzu.

 

Wannan aiki na daga cikin kokarin Gwamna Idris na inganta rayuwar al’umma a fadin jihar Kebbi.

 

Kwanan nan ya kaddamar da aikin gina hanyoyin karkara a babbar hanyar Yauri/Hundeji da ke karamar hukumar Shanga.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama
Manyan Labarai

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Labarai

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa
Labarai

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Next Post
Yadda Ake Kula Da Jama’a Ya Fi Muhimmanci

Yadda Ake Kula Da Jama'a Ya Fi Muhimmanci

LABARAI MASU NASABA

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.