• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Yi Gargaɗi Kan Yanke Wa Ma’aikata Kuɗi Ba Bisa Ƙa’ida Ba

by Leadership Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Yi Gargaɗi Kan Yanke Wa Ma’aikata Kuɗi Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umurnin dakatar da duk wani nau’in cirar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba daga albashin ma’aikatan jihar.

 

Wannan ya biyo bayan da Ma’aikatan Zamfara suk koka tare da ƙorafe-ƙorafe da dama dangane cire-ciren kuɗi da ake yi musu a tsarin biyan albashin jihar.

  • Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Atamfar Haɗin Kan Ƙasa Da Tallafin Littafi 50,000 A Zamfara 
  • Kotu Ta Hana CBN Da Sauransu Yi Wa Kudaden Kananan Hukumomi Katsa-Landan

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ya fitar a Gusau, ya bayyana cewa umurnin da aka bayar ya haramta duk wani nau’in cirar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba da ake yi ta hanyar biyan albashin gwamnatin Jihar Zamfara.

 

Labarai Masu Nasaba

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “A cikin ƙudirinsa na tsaftace tsarin biyan albashin ma’aikatan jihar Zamfara don samun ingantaccen tsarin biyan albashin su a adaidai lokacin da suke fuskantar cire-ciren kuɗi ba bisa ƙa’ida ba, Gwamna Dauda Lawal ya bayar da umarnin dakatar da duk wasu bangarori da ba sa bin doka da oda wajen zaftare wani sashi daga albashin ma’aikata.

 

“An yanke hukuncin ne saboda ƙorafe-ƙorafen da ake yi na cire-ciren kuɗi daga albashin ma’aikata, inda ake zaftare wasu kuɗaɗen da sunan wasu ƙungiyoyin haɗin gwiwa na ‘Cooperatives’, wasu kuma da sunan biyan wasu basukan kayayyaki.

 

“Gwamna Lawal ya umurci kwamishinan kuɗi da ya dakatar da duk irin wannan cire-cire daga albashin ma’aikata tare da isar da umarnin ga duk ƙungiyoyin haɗin gwiwa da sauran masu sayar da kayayyaki.

 

“Don ƙarin haske, bangarorin da aka yarda kaɗai su cire kuɗi su ne: PAYE; Kuɗin ƙungiya; NHF; ZAMCHEMA; kuɗin amfani da ruwa; FMB (Hayar Gida kafin Mallaka); FMB (Gyarar Gida); Kuɗin hannun jari.

 

“Gwamnatin da ke yanzu a jihar Zamfara ta himmatu wajen aiwatar da matakan da za su taimaka wa walwala da ci gaban ma’aikatan ta. Wannan ya haɗa da haɓaka yanayin aiki, samar da albarkatun da suka dace, da kuma samar da yanayi mai kyau don tabbatar da ƙwararewar ma’aikata wajen gudanar da ayyukan su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Cibiyar Horo Ta Sin Da Afrika Da MDD Domin Inganta Ci Gaba Nahiyar Afrika

Next Post

Nijeriya Za Ta Kara Haɓaka Alaƙarta Da Sabon Zaɓaɓɓen Shugaban Amurka – Gwamnati

Related

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Labarai

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

4 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

5 hours ago
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
Labarai

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

6 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

7 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

8 hours ago
Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
Labarai

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

9 hours ago
Next Post
Amurka

Nijeriya Za Ta Kara Haɓaka Alaƙarta Da Sabon Zaɓaɓɓen Shugaban Amurka – Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.