• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Yi Gargaɗi Kan Yanke Wa Ma’aikata Kuɗi Ba Bisa Ƙa’ida Ba

by Leadership Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Yi Gargaɗi Kan Yanke Wa Ma’aikata Kuɗi Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umurnin dakatar da duk wani nau’in cirar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba daga albashin ma’aikatan jihar.

 

Wannan ya biyo bayan da Ma’aikatan Zamfara suk koka tare da ƙorafe-ƙorafe da dama dangane cire-ciren kuɗi da ake yi musu a tsarin biyan albashin jihar.

  • Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Atamfar Haɗin Kan Ƙasa Da Tallafin Littafi 50,000 A Zamfara 
  • Kotu Ta Hana CBN Da Sauransu Yi Wa Kudaden Kananan Hukumomi Katsa-Landan

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ya fitar a Gusau, ya bayyana cewa umurnin da aka bayar ya haramta duk wani nau’in cirar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba da ake yi ta hanyar biyan albashin gwamnatin Jihar Zamfara.

 

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “A cikin ƙudirinsa na tsaftace tsarin biyan albashin ma’aikatan jihar Zamfara don samun ingantaccen tsarin biyan albashin su a adaidai lokacin da suke fuskantar cire-ciren kuɗi ba bisa ƙa’ida ba, Gwamna Dauda Lawal ya bayar da umarnin dakatar da duk wasu bangarori da ba sa bin doka da oda wajen zaftare wani sashi daga albashin ma’aikata.

 

“An yanke hukuncin ne saboda ƙorafe-ƙorafen da ake yi na cire-ciren kuɗi daga albashin ma’aikata, inda ake zaftare wasu kuɗaɗen da sunan wasu ƙungiyoyin haɗin gwiwa na ‘Cooperatives’, wasu kuma da sunan biyan wasu basukan kayayyaki.

 

“Gwamna Lawal ya umurci kwamishinan kuɗi da ya dakatar da duk irin wannan cire-cire daga albashin ma’aikata tare da isar da umarnin ga duk ƙungiyoyin haɗin gwiwa da sauran masu sayar da kayayyaki.

 

“Don ƙarin haske, bangarorin da aka yarda kaɗai su cire kuɗi su ne: PAYE; Kuɗin ƙungiya; NHF; ZAMCHEMA; kuɗin amfani da ruwa; FMB (Hayar Gida kafin Mallaka); FMB (Gyarar Gida); Kuɗin hannun jari.

 

“Gwamnatin da ke yanzu a jihar Zamfara ta himmatu wajen aiwatar da matakan da za su taimaka wa walwala da ci gaban ma’aikatan ta. Wannan ya haɗa da haɓaka yanayin aiki, samar da albarkatun da suka dace, da kuma samar da yanayi mai kyau don tabbatar da ƙwararewar ma’aikata wajen gudanar da ayyukan su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Cibiyar Horo Ta Sin Da Afrika Da MDD Domin Inganta Ci Gaba Nahiyar Afrika

Next Post

Nijeriya Za Ta Kara Haɓaka Alaƙarta Da Sabon Zaɓaɓɓen Shugaban Amurka – Gwamnati

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

5 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

6 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

7 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

12 hours ago
Zamfara
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

12 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

13 hours ago
Next Post
Amurka

Nijeriya Za Ta Kara Haɓaka Alaƙarta Da Sabon Zaɓaɓɓen Shugaban Amurka – Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.