• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Umarci Mayar Da Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Shafa A Suleja Zuwa Manyan Asibitoci

by Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Gwamnati Ta Umarci Mayar Da Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Shafa A Suleja Zuwa Manyan Asibitoci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin gaggawa na tura mutanen da suka jikkata a hatsarin fashewar tankar man fetur da ya faru a Suleja, Jihar Neja, daga Asibitin Suleja zuwa manyan asibitoci domin samun ingantacciyar kulawar lafiya cikin sauri.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan yayin wata ziyara da ya kai Suleja a ranar Lahadi.

  • Tinubu Ya Himmatu Wajen Kammala Titin Abuja Zuwa Kano Cikin Watanni 14 – Minista
  • TikTok Ya Dawo Aiki A Amurka Bayan Matakin Da Trump Ya Ɗauka 

Idris ya jagoranci wata tawaga daga Gwamnatin Tarayya, ciki har da Ministan Harkokin Jinƙai da Rage Talauci, Dr. Nentawe Yilwatda, domin tantance halin da ake ciki da kuma miƙa ta’aziyyarsu ga Gwamnatin Jihar Neja da mazauna yankin bisa hatsarin da ya faru a Dikko Junction.

 

Labarai Masu Nasaba

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

“Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu yana cikin matuƙar jimami kan wannan mummunan al’amari. Ya umurce mu da mu zo nan don ganin halin da ake ciki. Mun zagaya ɗakin masu jinya, kuma mun ga waɗanda ke cikin mummunan hali. Muna nan ana duba su, amma abin takaici, ɗaya daga cikinsu ya rasu. Wannan shi ne mutum na takwas da ya rasu sakamakon wannan hatsari. Gwamnatin Tarayya za ta tabbatar da cewa an yi gaggawar tura waɗannan mutanen da suka jikkata zuwa manyan asibitoci,” inji Idris.

 

Ministan ya yaba da gaggawar Gwamnatin Jihar Neja wajen bayar da taimakon gaggawa ga waɗanda suka jikkata.

 

Yayin da yake bayyana damuwarsa kan yawaitar fashewar tankar man fetur a ƙasar, inda mutane sama da 265 suka rasa rayukansu a cikin watanni biyar, Idris ya bayyana cewa Shugaban Ƙasa Tinubu ya kafa kwamiti domin bincikar musabbabin faruwar waɗannan al’amura da kuma samar da mafita don hana faruwar hakan a gaba.

 

“Shugaban ƙasa yana cikin damuwa sosai game da abin da ya faru. Ya kafa kwamitin bincike na musamman don gano musabbabin waɗannan abubuwan. A cikin watanni biyar da suka gabata, mun fuskanci manyan haɗura huɗu: ɗaya tsakanin Ibadan da Ife, wani a Agaie, Jihar Neja, inda mutane 48 suka rasa rayukansu, wani kuma a Jihar Jigawa inda mutane 144 suka mutu, sannan wannan a Suleja inda kusan mutane 80 suka mutu. Idan aka haɗa yawan waɗanda suka rasa rayukansu, sama da mutane 265 ne suka mutu a irin waɗannan haɗurra.

 

“Kwamitin da aka kafa, wanda ya ƙunshi manyan ma’aikatu da hukumomi kamar Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, NEMA, FRSC, NUPRC, da NARTO, zai binciki musabbabin haɗurran tare da bayar da shawarwari don hana sake faruwar su,” inji Idris.

 

Ministan ya ce, a bisa umarnin da Shugaban Ƙasa ya bayar kwanan nan, Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Ƙasa (NOA) za ta ƙara himma wajen wayar da kan jama’a kan haɗarin kwasan man fetur daga tankokin mai da suka yi hatsari domin hana aukuwar irin waɗannan al’amura nan gaba. Ya yi tir da wannan ɗabi’a, yana mai bayyana ta a matsayin abin da ba za a yarda da shi ba.

 

Tawagar ta fara kai ziyara ta jaje ga Sarkin Suleja, Alhaji Auwal Ibrahim, sannan ta ziyarci waɗanda suka jikkata a Asibitin Suleja da wurin da haɗarin ya faru.

 

Sauran waɗanda suka kasance a tawagar har da Daraktocin Janar na Gidan Talabijin na Nijeriya (NTA), Abdulhamid Dembos; Muryar Nijeriya (VON), Jibrin Baba Ndace; da Rediyon Tarayya na Nijeriya (FRCN), Mohammed Bulama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Sace Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki 18 A Cikin Kwanaki 6 – TCN

Next Post

Bidiyon Rashin Ɗa’a: Hukumar Tace Fina-finai Ta Dakatar Da Soja-boy Daga Shiga Duk Wata Harka Ta Kannywood

Related

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

44 minutes ago
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

12 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

13 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

14 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

17 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

18 hours ago
Next Post
Bidiyon Rashin Ɗa’a: Hukumar Tace Fina-finai Ta Dakatar Da Soja-boy Daga Shiga Duk Wata Harka Ta Kannywood

Bidiyon Rashin Ɗa'a: Hukumar Tace Fina-finai Ta Dakatar Da Soja-boy Daga Shiga Duk Wata Harka Ta Kannywood

LABARAI MASU NASABA

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.