• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Za Ta Goyi Bayan Shirin Fim Kan Tarihin Shekaru 25 Na Dimokuraɗiyyar Nijeriya

by Sulaiman
5 months ago
in Labarai
0
Gwamnati Za Ta Goyi Bayan Shirin Fim Kan Tarihin Shekaru 25 Na Dimokuraɗiyyar Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa za ta ba da cikakken goyon baya ga samar da wani shirin fim mai nuna tarihin shekaru 25 na mulkin dimokiraɗiyya a Nijeriya.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a lokacin da ya karɓi baƙuncin shugabannin Majalisar Tuntuɓa ta Jam’iyyun Siyasa, wato Inter-Party Advisory Council (IPAC), a ranar Juma’a a Abuja.

  • Kalaman Lai Chin-te Na Shan Suka A Fadin Taiwan
  • NPA Za Ta Yunkuro Don Zamanantar Da Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya – Dantsoho

Daraktan Yaɗa Labarai a ma’aikatar, Dakta Suleiman Haruna,ya faɗa a takarda ga manema labarai cewa Idris ya bayyana fim ɗin, wanda IPAC ce ta yi tunanin a shirya shi, a matsayin muhimmin tarihin tafiyar da dimokiraɗiyyar Nijeriya ta yi a cikin shekaru 25 da suka gabata.

 

Labarai Masu Nasaba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

Ya ce fim ɗin tarihin zai nuna nasarori, ƙalubale, da darussan da aka koya a wannan tafiya.

 

Ya ce: “Na yi farin cikin ganin ƙoƙarin da IPAC da shugabannin ta suke yi wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya, musamman ta hanyar fim ɗin wanda zai zama wata muhimmiyar shaida ta tarihi, domin girmama jaruman siyasar ƙasar mu da kuma nuna jajircewar Nijeriya a harkar dimokiraɗiyya. A kan haka, Gwamnatin Tarayya, ta hannun Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, za ta goyi bayan shirya wannan fim na musamman.”

 

Ya jinjina wa IPAC kan jajircewar ta wajen cigaban dimokiraɗiyya tare da jaddada muhimmancin haɗin kan jam’iyyun siyasa bayan zaɓe domin ƙarfafa haɗin kan ƙasa da cigaba.

 

“Gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tana goyon bayan a yi gasa mai kyau a siyasa, domin dimokiraɗiyya tana bunƙasa ne idan ana samun hamayya mai ma’ana da haɗin kai bisa muradin ƙasa ba tare da la’akari da bambancin jam’iyyun siyasa ba,” inji Idris.

 

Ya ƙara da cewa ɗorewar tsarin dimokiraɗiyya tana buƙatar haɗin gwiwa daga kowane ɓangare.

 

Ya ce: “Jam’iyyun siyasa su ne ginshiƙin dimokiraɗiyya; kuma yayin da hamayya take da muhimmanci a lokacin zaɓe, dole ne mu haɗa kai bayan haka don gina ƙasar mu.

 

“Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, wanda babban ɗan dimokiraɗiyya ne, yana mutunta gasa mai tsafta, amma yana kuma fifita haɗin kai da cigaban ƙasa.”

 

Shugaban IPAC na ƙasa, Honourable Yusuf Ɗantalle, ya ce shirin fim ɗin tarihin zai bayyana cigaban da aka samu a fannonin gina ababen more rayuwa, kiwon lafiya, ilimi, da haɗin kan al’umma.

Fim

Ɗantalle ya ce: “Fim ɗin, a matsayin wani muhimmin tarihin ƙasa, zai mayar da hankali kan matasa, musamman ‘yan zamani (Gen Z), domin ya zama wata hanyar ilmantarwa da haɗe kan ‘yan ƙasa kan tafiyar dimokiraɗiyyar Nijeriya. Fim ɗin zai ƙunshi fitattun jaruman Nollywood kuma za a shirya shi da na’urori na zamani domin ya dace da matakin inganci na duniya.”

 

Daga cikin shugabannin IPAC da suka halarci taron akwai Mataimakin Ciyaman ɗin IPAC na Ƙasa Dipo Olayokun, da memba a majalisar, Cif Dan Nwayanwu, da Sakatare na Ƙasa, Maxwell Mabudem.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jim Ratcliffe Ya Ce Zai Iya Barin Manchester United Idan Aka Ci Gaba Da Cin Zarafinsa

Next Post

Kasar Sin Na Adawa Da Zarge-Zargen G7 Don Gane Da Tekun Kudancin Kasar

Related

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da ɗumi-ɗuminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

2 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas
Manyan Labarai

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

4 hours ago
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa
Labarai

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

6 hours ago
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

7 hours ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

9 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

18 hours ago
Next Post
Kasar Sin Na Adawa Da Zarge-Zargen G7 Don Gane Da Tekun Kudancin Kasar

Kasar Sin Na Adawa Da Zarge-Zargen G7 Don Gane Da Tekun Kudancin Kasar

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

August 26, 2025
Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

August 26, 2025
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.