• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Ta Nisanta Kanta Akan Bidiyon Dukan Dan Balki Kwamanda

by Sulaiman and Shehu Yahaya
1 year ago
Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta bayar da Umarnin gudanar da cikakken bincike kan Bidiyon dukan Abdulmajid dan Bilki Kwamanda, wanda yake yawo a kafafen sada zumunta.

A wata sanawar da aka rabawa manema labarai mai dauke da sa hannun babban sakataren yada labarai na gwamnatin jihar Kaduna, Muhammad Lawal Shehu, yace gwamnatin ta nisanta kanta akan lamarin.

  • Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnatin Tarayya Da Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Amince A Kan N70,000 Mafi Ƙarancin Albashi
  • Malamin Tsangaya Ya Shiga Hannu Kan Zargin Luwadi Da Ɗalibai A Jigawa

“An ja hankalin gwamnatin jihar Kaduna game da wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta, inda aka nuna wasu da ba’ a san ko su wanene ba su na yi wa dan Bilki Kwamanda bulala bisa zargin shi da zagin gwamna Uba Sani”

Sanarwar ta ci gaba da cewa “Gwamnatin jihar Kaduna dai ta nisanta kan ta daga mummunan lamarin, ta na mai cewa, hakan ba ya da hurumi a duk wata al’umma tagari, don haka ta na nan a kan bakan ta na mutunta tsarin bin doka da oda.”

Haka kuma, gwamnatin jihar Kaduna ta ce, tsarin shugabancinta an gina shi ne a kan adalici da daidaito da kuma mutunta dan Adam.

LABARAI MASU NASABA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

Kaduna
Dan Balki Kwamanda

Sanarwar ta kara da cewa, gwamnatin jihar Kaduna ta na maraba da shawarwarin al’umma, sannan ta bude kofar da kowa zai iya bayyana ra’ayinsa a siyasance.

Ta ce Gwamnan jihar Kaduna ya kwashe tsawon lokaci ya na fafutukar kare ‘yancin dan Adam, don haka, har yanzu ya na kan bakan shi na tabbatar da ganin ba a tauye hakkin kowane bil-Adama ba bisa tsarin doka da oda.

Tuni dai Gwamna Uba Sani ya bada umurnin a gudanar da kwakkwaran bincike a kan mumman lamarin, sannan ya lashi takobin bin diddigin yadda lamarin ya faru, tare da bada tabbacin cewa duk mai hannu a aika-aikar dole ya fuskanci hukuncin abin da ya aikata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi
Manyan Labarai

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal
Labarai

Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

November 8, 2025
Next Post
Sin Ta Kaddamar Da Tallace-Tallacen Yawon Bude Ido Na Lokacin Zafi Don Karfafa Sayayya

Sin Ta Kaddamar Da Tallace-Tallacen Yawon Bude Ido Na Lokacin Zafi Don Karfafa Sayayya

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

November 8, 2025
Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Yadda Ake Miyar Margi

Yadda Ake Miyar Margi

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

November 8, 2025
Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Maganin Nankarwa (4)

Maganin Nankarwa (4)

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.