Majalisar gudanarwar kasar Sin, wato gwamnatin kasar ta zartas da wata ka’ida kan sanya ido sosai kan jama’a masu karamin karfi, da taimakon rukunonin al’umma, da shirye-shiryen ba da taimakon abinci ga tsoffi da kuma aiwatar da doka dangane da ‘yancin mallakar fasaha.
A cewar taron majalisar gudanarwar kasar wanda firaministan gwamnatin kasar Mr. Li Qiang ya jagoranta, ya kamata a yi kokarin ganin an samar da aikin ba da taimako ga jama’a yadda ya kamata, cikin sauri da inganci, don ganin an kyautata rayuwar jama’a. (Ibrahim Yaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp