Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Juma’a, 6, da Litinin, 9 ga watan Yuni, 2025, a matsayin ranakun hutu domin gudanar da bukukuwan Sallar Layya ta bana.
Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana hakan a madadin gwamnatin tarayya a cikin wata sanarwa da babbar sakatariyar ma’aikatar Dr Magdalene Ajani ta fitar ranar Litinin a Abuja.
Yayin da yake taya daukacin al’ummar Musulmi na gida da kuma na kasashen waje murnar wannan rana, ya yi kira gare su da su ci gaba da yin koyi da sadaukarwa da tausayi kamar yadda Annabi Ibrahim (A.S) ya yi, tare da yin amfani da wannan lokaci wajen yi wa Nijeriya addu’ar zaman lafiya da wadata.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp