• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Soke Kwangilar Gyaran Titin Abuja Zuwa Kaduna Da Kano

by Naziru Adam Ibrahim
8 months ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Tarayya Ta Soke Kwangilar Gyaran Titin Abuja Zuwa Kaduna Da Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta soke kwangilar da ta bai wa kamfanin Julius Berger na gyaran sashe na ɗaya na babbar titin Abuja zuwa Kaduna da Zariya zuwa Kano, saboda kin amincewa da farashin N740,797,204,173.25 da sauransu.

Daraktan Yada Labarai na Ma’aikatar Ayyuka Mohammed Ahmed, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar.

  • Kamfanin Google Ya Bai Wa Nijeriya Tallafin N2.8bn Don Bunkasa Tattalin Arziki
  • Yawan ‘Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Da Suka Halarci Canton Fair A Wannan Karo Ya Kafa Tarihi

Ya ce an dakatar da kwantiragin ne saboda rashin bin ka’idojin da aka yi bitarsu na biyan kuɗin da sauran sharudan aikin da suka hada da dakatar da aiki da kuma kin zuwa wurin don ci gaba.

Ya yi nuni da cewa ma’aikatar ayyuka ta bayar da sanarwar dakatar da kamfanin na Julius Berger, tsawon kwanaki 14 don gyaran babbar hanyar ta daga Abuja zuwa Kaduna da Zariya zuwa Kano kan kwangila mai lamba 6350.

Ma’aikatar ta yi amfani da sashe na dokokin kwangila wajen soke aikin a ranar 4 ga watan Nuwamba, 2024.

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

Ya bayyana cewa kwangilar gyaran hanyoyin ta kasu kashi uku ne, wanda an bai wa Julius Berger ne a ranar 20 ga watan Disambar 2017, inda aka fara a ranar 18 ga watan Yuni 2018, ta hannun ministan ayyuka da gidaje na lokacin, Babatunde Raji Fashola, a wanda ya fara biyan kudi N155.748,178,425.50, don soma aikin

Ya ce an kammala sashe na biyu na hanyar wato Kaduna zuwa Zariya, da na uku Zariya zuwa Kano, tare da miƙa su a lokacin gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari.

Ya ce ma’aikatar ta mika takardar buƙatar amincewar kamfanin na karshe game da aikin a ranar 23 ga watan Oktoba, 2024, tare da neman ya bayyana ra’ayinsa a rubuce, don karɓar kudin kwangilar da aka sake dubawa na N740,797,204,173.25 cikin kwanaki bakwai, ko kuwa ya rasa kwangilar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abuja-KadunaAikin HanyaJulius BergerKwangilaZariya-Kano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin Google Ya Bai Wa Nijeriya Tallafin N2.8bn Don Bunkasa Tattalin Arziki

Next Post

Yau Amurkawa Ke Kaɗa Ƙuri’ar Zaɓen Shugaban Ƙasa

Related

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

36 minutes ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

2 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

4 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

5 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

6 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

11 hours ago
Next Post
Yau Amurkawa Ke Kaɗa Ƙuri’ar Zaɓen Shugaban Ƙasa

Yau Amurkawa Ke Kaɗa Ƙuri'ar Zaɓen Shugaban Ƙasa

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.