• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fito Da Manhajar DSO Na Aikin Talbijin Kwanan Nan – Minista

by Sulaiman
2 years ago
DSO

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa ma’aikatarsa ta na nan ta na aiki tuƙuru domin fito da sabuwar manhajar da za a yi amfani da ita wajen aikin talbijin a duk faɗin ƙasar nan, wato ‘Digital Switch Over’ (DSO).

Hadimin musamman kan harkar yaɗa labarai na ministan, Malam Rabi’u Ibrahim, ya bayyana a cikin wata takardar sanarwa da ya fitar cewa, ministan ya faɗi haka ne a Abuja a ranar Litinin a lokacin da ya ke buɗe babban taron sanin makamar aiki na shugabannin gudanarwa na Hukumar Talbijin ta Ƙasa (NTA).

  • An Sake Mayar Da Emefiele Gidan Yari Saboda Gaza Cika Sharudan Beli
  • Rikicin Shugabanci: PTD Ta Ce Kwamared Egbon Kawai Ta Sani A Kaduna

Ya ce: “Ina kuma so in yi amfani da wannan damar in nanata sadaukarwar Gwamnatin Tarayya ga tsarin ‘Digital Switch Over’, domin kuwa Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai ta na ta aiki tuƙuru kan manhajar DSO wadda ba za ta gaza ba; wadda za a yi amfani da ita a birane da ƙauyukan Nijeriya. Ana sa ran cewa hukumar NTA, a matsayin ta na babbar mai ruwa da tsaki a tsarin na DSO, za ta taka muhimmiyar rawa a ciki.”

Don haka Idris ya ƙalubalanci NTA da ta yi zuzzurfan tunani kan yadda yanayin aikin jarida ya ke sauyawa, musamman da yake sababbin fasahohin zamani na shigowa kuma zaɓin masu kallo shi ma ya na canzawa tare da kawo ƙalubale da kuma damarmaki.

Ya ce: “Sadaukarwar mu ga tabbatar da inganci da kuma karɓar sauyi shi ne gaba da komai. Tilas ne NTA ta ci gaba da rungumar canji, ta na karɓar sababbin dabaru a yayin da ta ke riƙe da darajar aikin jarida mafi girma sau da ƙafa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

“Wannan taron ya zo ne a daidai lokacin da masu kallo su ke ta samun zaɓi daban-daban na inda za su samu bayanai, musamman ma da yake yanzu soshiyal midiya na da ƙarfi tare da tasiri wajen yaɗa labaran ƙarya da yaudara da ke akwai a cikin ta; don haka muhimmancin taro irin wannan ba ƙarami ba ne.”

Ya lura da cewa ɗaga ƙarfin hotuna da sautin da aka samu a NTA daga matakin ‘standard definition’ (SD) zuwa matakin ‘high definition’ (HD) ya na yin tasiri matuƙa a wajen jama’a masu kallo, ya ƙara da cewa tilas ne a samar da wannan tsarin a dukkan tashoshin NTA da ke faɗin ƙasar nan idan ana so a cimma manufar da ake buƙata.

Dangane da batun Tsarin Sabuwar Fata (Renewed Hope Agenda) na gwamnatin Shugaba Tinubu kuwa, wanda ya bayyana da cewa ba a taɓa samun dabarar gina ƙasa ta ɓangaren zamantakewa da tattalin arziki a Nijeriya kamar ta ba, don haka a cewar Idris, “haƙƙi ya rataya a wuyan NTA ta ci gaba da wayar da kan ‘yan Nijeriya kan nasarorin da ake samu a dukkan ɓangarori, kuma ta tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya sun fahimci alƙiblar da gwamnatin Tinubu ta fuskanta wajen yaɗa labarai da tsara shirye-shiryen talbijin.

Ministan ya buƙaci NTA da ta dage wajen dawo da martabar da aka san ta da ita a baya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Majalisar Dattawa
Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Next Post
Sojoji Sun Gargadi Masu Zanga-Zanga A Nasarawa

Sojoji Sun Gargadi Masu Zanga-Zanga A Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.