• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fito Da Manhajar DSO Na Aikin Talbijin Kwanan Nan – Minista

bySulaiman
2 years ago
DSO

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa ma’aikatarsa ta na nan ta na aiki tuƙuru domin fito da sabuwar manhajar da za a yi amfani da ita wajen aikin talbijin a duk faɗin ƙasar nan, wato ‘Digital Switch Over’ (DSO).

Hadimin musamman kan harkar yaɗa labarai na ministan, Malam Rabi’u Ibrahim, ya bayyana a cikin wata takardar sanarwa da ya fitar cewa, ministan ya faɗi haka ne a Abuja a ranar Litinin a lokacin da ya ke buɗe babban taron sanin makamar aiki na shugabannin gudanarwa na Hukumar Talbijin ta Ƙasa (NTA).

  • An Sake Mayar Da Emefiele Gidan Yari Saboda Gaza Cika Sharudan Beli
  • Rikicin Shugabanci: PTD Ta Ce Kwamared Egbon Kawai Ta Sani A Kaduna

Ya ce: “Ina kuma so in yi amfani da wannan damar in nanata sadaukarwar Gwamnatin Tarayya ga tsarin ‘Digital Switch Over’, domin kuwa Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai ta na ta aiki tuƙuru kan manhajar DSO wadda ba za ta gaza ba; wadda za a yi amfani da ita a birane da ƙauyukan Nijeriya. Ana sa ran cewa hukumar NTA, a matsayin ta na babbar mai ruwa da tsaki a tsarin na DSO, za ta taka muhimmiyar rawa a ciki.”

Don haka Idris ya ƙalubalanci NTA da ta yi zuzzurfan tunani kan yadda yanayin aikin jarida ya ke sauyawa, musamman da yake sababbin fasahohin zamani na shigowa kuma zaɓin masu kallo shi ma ya na canzawa tare da kawo ƙalubale da kuma damarmaki.

Ya ce: “Sadaukarwar mu ga tabbatar da inganci da kuma karɓar sauyi shi ne gaba da komai. Tilas ne NTA ta ci gaba da rungumar canji, ta na karɓar sababbin dabaru a yayin da ta ke riƙe da darajar aikin jarida mafi girma sau da ƙafa.

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

“Wannan taron ya zo ne a daidai lokacin da masu kallo su ke ta samun zaɓi daban-daban na inda za su samu bayanai, musamman ma da yake yanzu soshiyal midiya na da ƙarfi tare da tasiri wajen yaɗa labaran ƙarya da yaudara da ke akwai a cikin ta; don haka muhimmancin taro irin wannan ba ƙarami ba ne.”

Ya lura da cewa ɗaga ƙarfin hotuna da sautin da aka samu a NTA daga matakin ‘standard definition’ (SD) zuwa matakin ‘high definition’ (HD) ya na yin tasiri matuƙa a wajen jama’a masu kallo, ya ƙara da cewa tilas ne a samar da wannan tsarin a dukkan tashoshin NTA da ke faɗin ƙasar nan idan ana so a cimma manufar da ake buƙata.

Dangane da batun Tsarin Sabuwar Fata (Renewed Hope Agenda) na gwamnatin Shugaba Tinubu kuwa, wanda ya bayyana da cewa ba a taɓa samun dabarar gina ƙasa ta ɓangaren zamantakewa da tattalin arziki a Nijeriya kamar ta ba, don haka a cewar Idris, “haƙƙi ya rataya a wuyan NTA ta ci gaba da wayar da kan ‘yan Nijeriya kan nasarorin da ake samu a dukkan ɓangarori, kuma ta tabbatar da cewa ‘yan Nijeriya sun fahimci alƙiblar da gwamnatin Tinubu ta fuskanta wajen yaɗa labarai da tsara shirye-shiryen talbijin.

Ministan ya buƙaci NTA da ta dage wajen dawo da martabar da aka san ta da ita a baya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Sojoji Sun Gargadi Masu Zanga-Zanga A Nasarawa

Sojoji Sun Gargadi Masu Zanga-Zanga A Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version