• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

by Sulaiman
3 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Zamfara ta ƙaryata zargin da ake na cewa Gwamna Lawal ya ciyo bashin kuɗi, inda ta bayyana irin waɗannan ikirari a matsayin wani mummunan hali na Sahara Reporters.

 

A ranar Litinin da ta gabata ne Sahara Reporters ta buga wani labari mai taken ‘RAHOTON MUSAMMAN: Takardun Kasafin Kuɗi Sun Fallasa Ikirarin Ƙarya Da Gwamnan Zamfara Lawal Ya Yi Na Rashin Karbar Lamuni — An Karbi Bashin Naira Biliyan 34 A Ƙarƙashin Gwamnatinsa’.

  • Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba
  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris ya fitar a Gusau, ya bayyana Sahara Reporters a matsayin kafar yaɗa labarai ta yanar gizo da ke jin daɗin yaɗa labaran ƙarya.

 

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Sanarwar ta ƙara da cewa, aikin Sahara ba wai kawai aikin jaridar bogi ba ne; ya samo asali ne zuwa da suna ‘Gonzo’, wanda ke da alaƙa da ƙarairayi wajen bayar da rahoto.

 

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “An ja hankalinmu kan labaran ƙarya da Sahara Reporters ke yaɗawa, shafin da ya shahara wajen yaɗa labaran ƙarya domin tayar da ƙura a intanet.

 

“A yayin tattaunawa da manema labarai kai tsaye a makon da ya gabata, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana ƙudirinsa na ɗaukar nauyin kasafin kuɗi, inda ya tabbatar da cewa bai karbi lamuni na cikin gida ko na ƙasashen waje ba tsawon shekaru biyu da ya yi yana mulki.

 

“Amma abin ya ba mu mamaki, manyan jami’an yaɗa labaran ƙarya, Sahara Reporters, sun wallafa abin da suka sanya a matsayin wani rahoto na musamman na yadda aka karbi rancen Naira Biliyan 34 a ƙarƙashin kulawar Gwamna Lawal.

 

“Rahoton na Sahara ya bayyana ƙarara irin gazawar su wajen neman ƙwararan bayanai tare da yin nazari kan takardar kasafin kuɗin jihar Zamfara.

 

“Rahoton lamuni na naira biliyan 34 da Sahara Reporters ta yaɗa na buƙatar ƙarin haske domin tabbatar da cewa jama’a sun fahimci gaskiyar lamarin.

 

“An shirya Kasafin Kuɗi na 2023 ne a zamanin gwamnatin Bello Matawalle, wanda a yanzu shi ne Ƙaramin Ministan Tsaro, daga cikin kasafin kuɗin, an ware biliyan 53.2 domin kula da lamuni da gwamnatin jihar ta karbo.

 

“Duk da cewa ba a samu lamuni a wannan adadi na sama ba, gwamnatin jihar Zamfara ta kashe biliyan 34 wajen biyan kuɗin ruwa na rance daban-daban da gwamnatocin baya suka karba, hakan ya nuna yadda Dauda Lawal ya jajirce wajen rage yawan bashin da ake bin Zamfara da kuma hana karbar ƙarin lamuni.

 

“Duk dandali da ya ƙuduri aniyar yin aikin jarida na gaskiya zai gudanar da cikakken bincike don tabbatar da hasashensa da kuma tabbatar da sahihancin sa, amma Sahara Reporters ta zabi wata hanya ta daban, ta tsaya kan tsarin aikin jaridar bogi.

 

“Ya kamata Sahara Reporters ta tambayi tsohon Gwamna Bello Matawalle kan yadda ya yi amfani da lamunin da ya karba a zamaninsa, wanda hakan bai haifar da wani ci gaba ba, rancen da muke biya kenan.

 

“Gwamna Dauda Lawal bai karbi rance ba tsawon shekaru biyu da ya yi yana Gwamnan jihar Zamfara.

 

“Muna ƙalubalantar Sahara Reporters da su samar da duk wasu takardun da ke nuna gwamnatin Zamfara mai ci na neman lamuni, ko a cikin gida ko kuma a waje.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Next Post

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Related

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Labarai

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

5 hours ago
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

8 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

8 hours ago
Zamfara
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

10 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

12 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

12 hours ago
Next Post
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Zamfara

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.