• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

by Sulaiman
1 month ago
in Labarai
0
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Zamfara ta ƙaryata zargin da ake na cewa Gwamna Lawal ya ciyo bashin kuɗi, inda ta bayyana irin waɗannan ikirari a matsayin wani mummunan hali na Sahara Reporters.

 

A ranar Litinin da ta gabata ne Sahara Reporters ta buga wani labari mai taken ‘RAHOTON MUSAMMAN: Takardun Kasafin Kuɗi Sun Fallasa Ikirarin Ƙarya Da Gwamnan Zamfara Lawal Ya Yi Na Rashin Karbar Lamuni — An Karbi Bashin Naira Biliyan 34 A Ƙarƙashin Gwamnatinsa’.

  • Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba
  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris ya fitar a Gusau, ya bayyana Sahara Reporters a matsayin kafar yaɗa labarai ta yanar gizo da ke jin daɗin yaɗa labaran ƙarya.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

Sanarwar ta ƙara da cewa, aikin Sahara ba wai kawai aikin jaridar bogi ba ne; ya samo asali ne zuwa da suna ‘Gonzo’, wanda ke da alaƙa da ƙarairayi wajen bayar da rahoto.

 

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “An ja hankalinmu kan labaran ƙarya da Sahara Reporters ke yaɗawa, shafin da ya shahara wajen yaɗa labaran ƙarya domin tayar da ƙura a intanet.

 

“A yayin tattaunawa da manema labarai kai tsaye a makon da ya gabata, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana ƙudirinsa na ɗaukar nauyin kasafin kuɗi, inda ya tabbatar da cewa bai karbi lamuni na cikin gida ko na ƙasashen waje ba tsawon shekaru biyu da ya yi yana mulki.

 

“Amma abin ya ba mu mamaki, manyan jami’an yaɗa labaran ƙarya, Sahara Reporters, sun wallafa abin da suka sanya a matsayin wani rahoto na musamman na yadda aka karbi rancen Naira Biliyan 34 a ƙarƙashin kulawar Gwamna Lawal.

 

“Rahoton na Sahara ya bayyana ƙarara irin gazawar su wajen neman ƙwararan bayanai tare da yin nazari kan takardar kasafin kuɗin jihar Zamfara.

 

“Rahoton lamuni na naira biliyan 34 da Sahara Reporters ta yaɗa na buƙatar ƙarin haske domin tabbatar da cewa jama’a sun fahimci gaskiyar lamarin.

 

“An shirya Kasafin Kuɗi na 2023 ne a zamanin gwamnatin Bello Matawalle, wanda a yanzu shi ne Ƙaramin Ministan Tsaro, daga cikin kasafin kuɗin, an ware biliyan 53.2 domin kula da lamuni da gwamnatin jihar ta karbo.

 

“Duk da cewa ba a samu lamuni a wannan adadi na sama ba, gwamnatin jihar Zamfara ta kashe biliyan 34 wajen biyan kuɗin ruwa na rance daban-daban da gwamnatocin baya suka karba, hakan ya nuna yadda Dauda Lawal ya jajirce wajen rage yawan bashin da ake bin Zamfara da kuma hana karbar ƙarin lamuni.

 

“Duk dandali da ya ƙuduri aniyar yin aikin jarida na gaskiya zai gudanar da cikakken bincike don tabbatar da hasashensa da kuma tabbatar da sahihancin sa, amma Sahara Reporters ta zabi wata hanya ta daban, ta tsaya kan tsarin aikin jaridar bogi.

 

“Ya kamata Sahara Reporters ta tambayi tsohon Gwamna Bello Matawalle kan yadda ya yi amfani da lamunin da ya karba a zamaninsa, wanda hakan bai haifar da wani ci gaba ba, rancen da muke biya kenan.

 

“Gwamna Dauda Lawal bai karbi rance ba tsawon shekaru biyu da ya yi yana Gwamnan jihar Zamfara.

 

“Muna ƙalubalantar Sahara Reporters da su samar da duk wasu takardun da ke nuna gwamnatin Zamfara mai ci na neman lamuni, ko a cikin gida ko kuma a waje.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Next Post

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Related

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno

1 hour ago
Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
Ra'ayi Riga

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

2 hours ago
Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa
Labarai

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

4 hours ago
Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno
Labarai

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

5 hours ago
Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno
Labarai

Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

8 hours ago
Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu
Labarai

Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

9 hours ago
Next Post
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

LABARAI MASU NASABA

Sai Ƴan Siyasa Sun Haɗa Kansu Sannan Za Su Iya Tunkarar APC A 2027 – Lukman

Sai Ƴan Siyasa Sun Haɗa Kansu Sannan Za Su Iya Tunkarar APC A 2027 – Lukman

August 8, 2025
Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

August 8, 2025
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno

August 8, 2025
UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari

UEFA Ta Ci Tarar Lamine Yamal Da Lewandowski Kan Karya Dokar Shan Ƙwayar Ƙara Kuzari

August 8, 2025
Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

August 8, 2025
Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

Ba Gaskiya Ba Ne Rahoton Da Ke Cewa An Yi Sulhu Da Bello Turji – Guyawa Isa

August 8, 2025
Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

August 8, 2025
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

August 8, 2025
GORON JUMA’A 8-8-2025

GORON JUMA’A 8-8-2025

August 8, 2025
Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.