• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nan da kasa da mako daya, gwamnoni 20 za su gudanar da bikin cika shekara daya a karagar mulki. Wasu daga cikinsu sun samu nasarar zama gwamnoni ne bisa goyon bayan ubanen gidansu wadanda suka share musu hanya.

A Nijeriya, babewa tsakanin ubangidan siyasa da yaronsa ba sabon abu ba ne.
Wasu daga cikin wadanda suka babe a siyasa sun hada da Rabiu Kwankwaso da Umar Ganduje, Peter Obi da Willie Obiano, Udom Emmanuel da Godswill Akpabio, Adams Oshiomhole da Godwin Obaseki, Rauf Aregbesola da Gboyega Oyetola, da dai sauransu.

A daya bangaren kuma, kila za a iya cewa Shugaban kasa, Bola Tinubu shi ne ubangidan siyasa da ya fi samun nasara a wannan komawa mulkin dimokuradiyya. Tsakanin 2007 har zuwa yau, ya kafa gwamnoni har guda uku a Jihar Legas, amma har zuwa yanzu shi ke rike da tsarin siyasar jihar.

A ‘yan kwanakin nan, rikici ya kara kamari tsakanin Gwamnan Jihar Ribas, Similayi Fubara da maigidansa da ya gada, Nyeson Wike.

Haka ma lamarin yake a Jihar Kaduna, inda a yanzu haka akwai alaman rikici tsakanin tsohon gwamna, Nasiru el-Rufai da Gwamna Uba Sani. A Jihar Benuwai ma lamarin ba ta sauya zani ba, inda Gwamna Alia da tsohon gwamna, George Akume suke kai rikici kan wanda zai zama jagoran jam’iyya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Haka zalika, akwai jihohin wasu jihohi da har yau ba a samu sabani tsakanin gwamna mai ci da kuma wanda ya gada. Ko da yake za a iya samun rikicin, amma bai kai ga har a buga a jaridu ba.
Kebbi

Tsohon gwamna, Atiku Bagudu ya goyi bayan Nasir Idris lokacin zaben fitar da gwani, wanda ya doke tsohon shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa, Yahaya Abdullahi.

Kusan shekara daya da kafuwar wannan gwamnati, Bagudu yana daga cikin manyan ministocin gwamnatin Tinubu, wanda har yanzu ba a samu hayaniya ba tsakaninsa da magajinsa kan shugabancin jihar.

Kano
Bayan da ya tsallake rijiya da baya na tsawon shekaru 8 a siyasar magajinsa, tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Kwankwaso ya zama ubangidan siyasa.

A 2019, Kwankwaso ya yi kokarin dora sirikinsa, Abba Yusuf kan mulkin Jihar Kano, amma bai yi nasara ba. Sai dai a 2023, Kwankwaso ya samu nasarar dora sirikinsa kan karagar mulkin Kano, wanda har yau ba a ji sun samu wani rashin fahimta ba.

Jigawa
Har zuwa yau ba a samu rikici ba tsakanin ministan tsaro kuma tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Abubakar Badaru da magajinsa, Umar Namadi ba.
Kamar dai sauran gwamnoni, Badaru shi ya zabi mataimakinsa a matsayin wanda zai gaje shi.
Idan za a iya tunawa, Namadi bai fara gwamnati da Badaru a 20015, ya shiga gwamnati ne lokacin da aka yada Ibrahim Hadeja a 2019.

Sakkwato

Aliyu Wamakko ya kasance cikin shugabancin Jihar Sakkwato tun daga 1999, lokacin da ya zama mataimakin tsohon gwamnan jihar, Attahiru Baffarawa.
Ya goyi bayan Aminu Tambuwal a 2015, amma sun samu rashin jituwan siyasa na wani dan lokaci, inda a bara ya sake goyon bayan Gwamna Ahmad Aliyu.
Har dai zuwa yanzu ba a ji rashin jituwar siyasar a tsakaninsu ba.

Akwa Ibom
Har zuwa yau ba a samu rikicin siyasa tsakanin tsohon gwamnan Jihar Akwa Ibom, Udom Emmanuel da Gwamna mai ci, Umo Eno ba.

Ebonyi

Tsohon gwamnan Jihar Ebonyi kuma ministan ayyuka, Dabe Umahi bai samu rikicin siyasa da shi da maganjinsa, Francis Nwifuru. A daidai lokacin da Umahi ke gudanar da ayyukan da suka shafi tarayya, shi kuwa gwamnan yana tafiyar da ayyukansa na jiha.

Kuros Ribas

Gwamna Bassey Out da ubangidansa, Ben Ayade suna da kyakkyawan danganta wajen gudanar da ayyuka tun bayan kammala zaben bara.

Inugu

Tsohon gwamnan Jihar Inugu, Ifeanyi Ugwuanyi ya goyi bayan, Peter Mbah gabanin zaben fitar da gwani na jam’iyyar PDP a 2022, duk da matsinlambar jam’iyyar LP, har zuwa yanzu dai PDP ke mulki a jihar.
Ugwuanyi ya kasa samun damar shiga majalisar dattawa, sakamakon turjiya daga dan takarar jam’iyyar LP, Okechukwu Ezea.
Sai dai har zuwa yanzu akwai kyakkyawan fahimta tsakanin tsohon gwamnan da kuma wanda ya gaje shi.

Delta
A 2023, a karon farko, dan takarar da James Ibori ya mara wa baya a zaben gwamnan Jihar Delta bai samu nasara ba.
Tsohon gwamnan jihar, Ifeanyi Okowa ya mara wa, Sheriff Oborebwori baya, wanda ya samu nasarar kayar da dan takarar Ibori, Dabid Edebbie.
Har dai zuwa yanzu ba a samu rikici tsakanin tsohon gwamnan da magajinsa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGwamantin Tinubusiyasar Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Fara Aikin Gina Yankin Masana’antun Jigilar Hajoji Dake Tashar Lekki Ta Najeriya

Next Post

An Shawarci Sarki Aminu Ado Ya Fice Daga Kano

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

7 hours ago
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
Labarai

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

8 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

10 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

12 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

15 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

15 hours ago
Next Post
An Shawarci Sarki Aminu Ado Ya Fice Daga Kano

An Shawarci Sarki Aminu Ado Ya Fice Daga Kano

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.