• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
gwamnoni

Nan da kasa da mako daya, gwamnoni 20 za su gudanar da bikin cika shekara daya a karagar mulki. Wasu daga cikinsu sun samu nasarar zama gwamnoni ne bisa goyon bayan ubanen gidansu wadanda suka share musu hanya.

A Nijeriya, babewa tsakanin ubangidan siyasa da yaronsa ba sabon abu ba ne.
Wasu daga cikin wadanda suka babe a siyasa sun hada da Rabiu Kwankwaso da Umar Ganduje, Peter Obi da Willie Obiano, Udom Emmanuel da Godswill Akpabio, Adams Oshiomhole da Godwin Obaseki, Rauf Aregbesola da Gboyega Oyetola, da dai sauransu.

A daya bangaren kuma, kila za a iya cewa Shugaban kasa, Bola Tinubu shi ne ubangidan siyasa da ya fi samun nasara a wannan komawa mulkin dimokuradiyya. Tsakanin 2007 har zuwa yau, ya kafa gwamnoni har guda uku a Jihar Legas, amma har zuwa yanzu shi ke rike da tsarin siyasar jihar.

A ‘yan kwanakin nan, rikici ya kara kamari tsakanin Gwamnan Jihar Ribas, Similayi Fubara da maigidansa da ya gada, Nyeson Wike.

Haka ma lamarin yake a Jihar Kaduna, inda a yanzu haka akwai alaman rikici tsakanin tsohon gwamna, Nasiru el-Rufai da Gwamna Uba Sani. A Jihar Benuwai ma lamarin ba ta sauya zani ba, inda Gwamna Alia da tsohon gwamna, George Akume suke kai rikici kan wanda zai zama jagoran jam’iyya.

LABARAI MASU NASABA

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

Haka zalika, akwai jihohin wasu jihohi da har yau ba a samu sabani tsakanin gwamna mai ci da kuma wanda ya gada. Ko da yake za a iya samun rikicin, amma bai kai ga har a buga a jaridu ba.
Kebbi

Tsohon gwamna, Atiku Bagudu ya goyi bayan Nasir Idris lokacin zaben fitar da gwani, wanda ya doke tsohon shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa, Yahaya Abdullahi.

Kusan shekara daya da kafuwar wannan gwamnati, Bagudu yana daga cikin manyan ministocin gwamnatin Tinubu, wanda har yanzu ba a samu hayaniya ba tsakaninsa da magajinsa kan shugabancin jihar.

Kano
Bayan da ya tsallake rijiya da baya na tsawon shekaru 8 a siyasar magajinsa, tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Kwankwaso ya zama ubangidan siyasa.

A 2019, Kwankwaso ya yi kokarin dora sirikinsa, Abba Yusuf kan mulkin Jihar Kano, amma bai yi nasara ba. Sai dai a 2023, Kwankwaso ya samu nasarar dora sirikinsa kan karagar mulkin Kano, wanda har yau ba a ji sun samu wani rashin fahimta ba.

Jigawa
Har zuwa yau ba a samu rikici ba tsakanin ministan tsaro kuma tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Abubakar Badaru da magajinsa, Umar Namadi ba.
Kamar dai sauran gwamnoni, Badaru shi ya zabi mataimakinsa a matsayin wanda zai gaje shi.
Idan za a iya tunawa, Namadi bai fara gwamnati da Badaru a 20015, ya shiga gwamnati ne lokacin da aka yada Ibrahim Hadeja a 2019.

Sakkwato

Aliyu Wamakko ya kasance cikin shugabancin Jihar Sakkwato tun daga 1999, lokacin da ya zama mataimakin tsohon gwamnan jihar, Attahiru Baffarawa.
Ya goyi bayan Aminu Tambuwal a 2015, amma sun samu rashin jituwan siyasa na wani dan lokaci, inda a bara ya sake goyon bayan Gwamna Ahmad Aliyu.
Har dai zuwa yanzu ba a ji rashin jituwar siyasar a tsakaninsu ba.

Akwa Ibom
Har zuwa yau ba a samu rikicin siyasa tsakanin tsohon gwamnan Jihar Akwa Ibom, Udom Emmanuel da Gwamna mai ci, Umo Eno ba.

Ebonyi

Tsohon gwamnan Jihar Ebonyi kuma ministan ayyuka, Dabe Umahi bai samu rikicin siyasa da shi da maganjinsa, Francis Nwifuru. A daidai lokacin da Umahi ke gudanar da ayyukan da suka shafi tarayya, shi kuwa gwamnan yana tafiyar da ayyukansa na jiha.

Kuros Ribas

Gwamna Bassey Out da ubangidansa, Ben Ayade suna da kyakkyawan danganta wajen gudanar da ayyuka tun bayan kammala zaben bara.

Inugu

Tsohon gwamnan Jihar Inugu, Ifeanyi Ugwuanyi ya goyi bayan, Peter Mbah gabanin zaben fitar da gwani na jam’iyyar PDP a 2022, duk da matsinlambar jam’iyyar LP, har zuwa yanzu dai PDP ke mulki a jihar.
Ugwuanyi ya kasa samun damar shiga majalisar dattawa, sakamakon turjiya daga dan takarar jam’iyyar LP, Okechukwu Ezea.
Sai dai har zuwa yanzu akwai kyakkyawan fahimta tsakanin tsohon gwamnan da kuma wanda ya gaje shi.

Delta
A 2023, a karon farko, dan takarar da James Ibori ya mara wa baya a zaben gwamnan Jihar Delta bai samu nasara ba.
Tsohon gwamnan jihar, Ifeanyi Okowa ya mara wa, Sheriff Oborebwori baya, wanda ya samu nasarar kayar da dan takarar Ibori, Dabid Edebbie.
Har dai zuwa yanzu ba a samu rikici tsakanin tsohon gwamnan da magajinsa ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 
Labarai

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Kotu
Manyan Labarai

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Asuu
Labarai

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Next Post
An Shawarci Sarki Aminu Ado Ya Fice Daga Kano

An Shawarci Sarki Aminu Ado Ya Fice Daga Kano

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Asuu

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.