• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa-Maso-Yamma Sun Nemi Goyon Bayan MDD Kan Magance Ƙalubalen Yankin

by Abdulrazaq Yahuza
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnonin Arewa-Maso-Yamma Sun Nemi Goyon Bayan MDD Kan Magance Ƙalubalen Yankin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnonin yankin Arewa maso Yamma na Nijeriya sun yi taro tare da tawagar Majalisar Dinkin Duniya, karkashin jagorancin mai kula da harkokin jin kai, Mohamed Malick Fall, a Abuja ranar Juma’a.

Manufar taron dai ita ce neman tallafi don tunkarar babban kalubalen ci gaban yankin.

  • IMF Ta Bayyana Dalilinta Na Neman Gwamnati Ta Janye Tallafin Lantarki
  • Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Da Su Zuba Jari Da Aiwatar Da Hada-hada A Kasar

Taron wanda Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa Maso Yamma kuma Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya jagoranta, ya samu halartar gwamnan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani, Injiniya Abba Kabir Yusuf na Kano, Mallam Umar Namadi na Jigawa; Mataimakin Gwamnan Sokoto, Alhaji Idris Muhammad Gobir, da Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal.

Taron wanda aka gudanar a zauren Majalisar Dinkin Duniya da ke Abuja, ya mayar da hankali ne kan batutuwan da suka shafi matsalolin tsaro, da talauci, da yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.

Gwamnonin sun kuma bayyana damuwarsu game da karuwar shan miyagun kwayoyi, yawan mace-macen yara da mata masu juna biyu, da rashin aikin yi ga matasa.

Labarai Masu Nasaba

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Sun qara bayyana tasirin kalubale kamar gurbacewar kasa da sauyin yanayi kan noma, wanda kusan kashi 80 na al’ummar kasar ke dogaro da su.

Bugu da kari, gwamnonin sun jaddada illar matsalar karancin abinci mai gina jiki ga lananan yara.

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa maso Yamma, ya jaddada buqatar samar da tsarin hadin kan yankin, inda ya ce, “Hanya daya da za mu iya shawo kan kalubalen Arewa maso Yamma ita ce hanyar da ake bi a yankin da ke bukatar mu hada kai ta hanyar haxin gwiwa. Ya kamata mu haxa karfi da karfe wajen yaki da talauci da rashin aikin yi, kasancewar manyan su abubuwan da ke haddasa rashin tsaro a yankin.”

Sai dai kuma Babban Jami’in Kula da Ayyukan Jin Kai na Majalisar Dinkin Duniya Mohamed Malick Fall, ya nuna farin cikinsa ga taron tare da tabbatar da aniyar Majalisar Dinkin Duniya na tallafa wa yankin na Arewa maso Yamma.

Ya bayyana muhimmancin rawar da yankin ke takawa wajen cimma muradun ci gaba mai dorewa (SDGs) a Nijeriya, wanda hakan zai amfani daukacin nahiyar Afirka.

“Majalisar Dinkin Duniya a Nijeriya tana da kwarin gwiwar ganin kwakkwaran jagoranci da jajircewar Gwamnonin Arewa maso Yamma na inganta rayuwar al’ummarsu. Za mu ci gaba da tallafa wa gwamnati da al’ummar Arewa maso Yammacin Nijeriya. Tare, za mu ceto da kuma hanzarta ajandar 2030 don ci gaba mai xorewa a yankin, “in ji Fall.

Fall ya kara sanar da gwamnonin game da yadda Majalisar Dinkin Duniya ta mayar da hankali wajen hanzarta cimma nasarar SDG ta fannoni shida: tsarin abinci, ilimi, kariyar zamantakewa da ayyukan yi, samar da makamashi, sauyin yanayi, da sauyi na dijital.

An kammala taron ne da yarjejeniyar samar da taswirar aiki, da tawagogin fasaha daga Majalisar Dinkin Duniya da na jihohi bakwai za su tsara, bisa tsarin tallafin Majalisar Dinkin Duniya ga yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnonin ArewaKalubaleMajalisar Dinkin Duniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

IMF Ta Bayyana Dalilinta Na Neman Gwamnati Ta Janye Tallafin Lantarki

Next Post

CBN Ya Yi Alkawarin Kawo Karshen Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

Related

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

7 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

9 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

11 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

11 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

14 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

16 hours ago
Next Post
CBN Ya Yi Alkawarin Kawo Karshen Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

CBN Ya Yi Alkawarin Kawo Karshen Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.