• English
  • Business News
Monday, May 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa-Maso-Yamma Sun Nemi Goyon Bayan MDD Kan Magance Ƙalubalen Yankin

by Abdulrazaq Yahuza
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnonin Arewa-Maso-Yamma Sun Nemi Goyon Bayan MDD Kan Magance Ƙalubalen Yankin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnonin yankin Arewa maso Yamma na Nijeriya sun yi taro tare da tawagar Majalisar Dinkin Duniya, karkashin jagorancin mai kula da harkokin jin kai, Mohamed Malick Fall, a Abuja ranar Juma’a.

Manufar taron dai ita ce neman tallafi don tunkarar babban kalubalen ci gaban yankin.

  • IMF Ta Bayyana Dalilinta Na Neman Gwamnati Ta Janye Tallafin Lantarki
  • Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Da Su Zuba Jari Da Aiwatar Da Hada-hada A Kasar

Taron wanda Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa Maso Yamma kuma Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya jagoranta, ya samu halartar gwamnan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani, Injiniya Abba Kabir Yusuf na Kano, Mallam Umar Namadi na Jigawa; Mataimakin Gwamnan Sokoto, Alhaji Idris Muhammad Gobir, da Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal.

Taron wanda aka gudanar a zauren Majalisar Dinkin Duniya da ke Abuja, ya mayar da hankali ne kan batutuwan da suka shafi matsalolin tsaro, da talauci, da yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.

Gwamnonin sun kuma bayyana damuwarsu game da karuwar shan miyagun kwayoyi, yawan mace-macen yara da mata masu juna biyu, da rashin aikin yi ga matasa.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Ƴan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutum 2

Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

Sun qara bayyana tasirin kalubale kamar gurbacewar kasa da sauyin yanayi kan noma, wanda kusan kashi 80 na al’ummar kasar ke dogaro da su.

Bugu da kari, gwamnonin sun jaddada illar matsalar karancin abinci mai gina jiki ga lananan yara.

Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa maso Yamma, ya jaddada buqatar samar da tsarin hadin kan yankin, inda ya ce, “Hanya daya da za mu iya shawo kan kalubalen Arewa maso Yamma ita ce hanyar da ake bi a yankin da ke bukatar mu hada kai ta hanyar haxin gwiwa. Ya kamata mu haxa karfi da karfe wajen yaki da talauci da rashin aikin yi, kasancewar manyan su abubuwan da ke haddasa rashin tsaro a yankin.”

Sai dai kuma Babban Jami’in Kula da Ayyukan Jin Kai na Majalisar Dinkin Duniya Mohamed Malick Fall, ya nuna farin cikinsa ga taron tare da tabbatar da aniyar Majalisar Dinkin Duniya na tallafa wa yankin na Arewa maso Yamma.

Ya bayyana muhimmancin rawar da yankin ke takawa wajen cimma muradun ci gaba mai dorewa (SDGs) a Nijeriya, wanda hakan zai amfani daukacin nahiyar Afirka.

“Majalisar Dinkin Duniya a Nijeriya tana da kwarin gwiwar ganin kwakkwaran jagoranci da jajircewar Gwamnonin Arewa maso Yamma na inganta rayuwar al’ummarsu. Za mu ci gaba da tallafa wa gwamnati da al’ummar Arewa maso Yammacin Nijeriya. Tare, za mu ceto da kuma hanzarta ajandar 2030 don ci gaba mai xorewa a yankin, “in ji Fall.

Fall ya kara sanar da gwamnonin game da yadda Majalisar Dinkin Duniya ta mayar da hankali wajen hanzarta cimma nasarar SDG ta fannoni shida: tsarin abinci, ilimi, kariyar zamantakewa da ayyukan yi, samar da makamashi, sauyin yanayi, da sauyi na dijital.

An kammala taron ne da yarjejeniyar samar da taswirar aiki, da tawagogin fasaha daga Majalisar Dinkin Duniya da na jihohi bakwai za su tsara, bisa tsarin tallafin Majalisar Dinkin Duniya ga yankin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnonin ArewaKalubaleMajalisar Dinkin Duniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

IMF Ta Bayyana Dalilinta Na Neman Gwamnati Ta Janye Tallafin Lantarki

Next Post

CBN Ya Yi Alkawarin Kawo Karshen Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

Related

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Ƴan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutum 2
Tsaro

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Ƴan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutum 2

4 hours ago
Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake
Labarai

Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

7 hours ago
Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota
Labarai

Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota

8 hours ago
Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa
Labarai

Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa

10 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Labarai

Tangarɗar Na’ura: JAMB Ta Sake Fitar Da Sakamakon Jarabawar UTME Ta 2025

12 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

Ya Kuɓuta A Hannun ‘Yan Bindiga Bayan Shafe Kwanaki 8 Yana Gudu A Dajin Sokoto Da Neja

12 hours ago
Next Post
CBN Ya Yi Alkawarin Kawo Karshen Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

CBN Ya Yi Alkawarin Kawo Karshen Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Ƴan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutum 2

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Ƴan Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Mutum 2

May 25, 2025
Fasahar Shayi Ta Sin Ta Samar Da Kwanciyar Hankali Da Nishadi Ga ‘Yan Nijeriya

Fasahar Shayi Ta Sin Ta Samar Da Kwanciyar Hankali Da Nishadi Ga ‘Yan Nijeriya

May 25, 2025
Chelsea, Man City, Newcastle Sun Samu Gurbi A Gasar Zakarun Turai Ta Baɗi

Chelsea, Man City, Newcastle Sun Samu Gurbi A Gasar Zakarun Turai Ta Baɗi

May 25, 2025
Xi Jinping Ya Taya Murnar Bude Bikin Baje Kolin Kayayyaki Na Yammacin Sin

Xi Jinping Ya Taya Murnar Bude Bikin Baje Kolin Kayayyaki Na Yammacin Sin

May 25, 2025
Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

Dabarun Tinubu Sun Ƙara Kuɗaɗe A Harkar Ma’adanai Daga Naira Biliyan 6 Zuwa Biliyan 38 — Alake

May 25, 2025
Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota

Fitaccen Fastan Kaduna Rabaran Azzaman Ya Mutu A Haɗarin Mota

May 25, 2025
Ruhin Yuan Longping Ya Ba Da Tabbaci Ga Samar Da Isashen Hatsi a Nahiyar Afirka

Ruhin Yuan Longping Ya Ba Da Tabbaci Ga Samar Da Isashen Hatsi a Nahiyar Afirka

May 25, 2025
Gasar Wasanni Ta Kasa: Jihar Binuwai Ta Samu Kyaututtuka 9 Zuwa Yanzu

Gasar Wasanni Ta Kasa: Jihar Binuwai Ta Samu Kyaututtuka 9 Zuwa Yanzu

May 25, 2025
Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa

Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa

May 25, 2025
An Kaddamar Da Babban Filin Wasan Da Kasar Sin Ta Gina Wa Kasar Chadi Kyauta

An Kaddamar Da Babban Filin Wasan Da Kasar Sin Ta Gina Wa Kasar Chadi Kyauta

May 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.