• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadarin Da Ya Auku Ya Bankado Karyar Japan Game Da Ruwan Dagwalon Nukiliyar Da Take Zubarwa A Teku

by CGTN Hausa
2 years ago
Teku

Duk da kakkarfar adawa daga gida da waje, kamfanin samar da lantarki na 2 na Tokyo ko TEPCO dake kasar Japan, ya fara zubar da ruwan dagwalon nukiliyar Fukushima cikin teku a zagaye na 3, aikin da ake fatan ci gaba da gudanarwa har zuwa ranar 20 ga watan nan na Nuwamba, kuma adadin ruwan da za a juye a wannan lokaci zai kai kusan tan 7,800.

Sai dai duk da haka, mako guda da ya gabata, kamfanin ya gamu da hadarin fitar birbishin “radioactive”, wanda ya jefa 2 daga cikin ma’aikatan kamfanin cikin hadari, aka kuma garzaya da su zuwa asibiti. Wannan lamari ya karyata ikirarin Japan, na cewa ruwan dagwalon da take zubarwa a teku ba shi da hadari, kuma bai dace a yi wasa da hadarin dake tattare da hadarin birbishin nukiliya dake cikin ruwan ba.

  • Kungiyar ‘One Germany’ Ta Fara Gangamin Samar Da Karin Masu Zuba Jari A Afirika
  • Xi Ya Gana Da Firaministan Girka Da Yin Tattaunawa Da Shugaban Gwamnatin Jamus

Bayan aukuwar wannan hadari, jami’an hukumar lura da sana’ar kamun kifi ta Fukushima, sun ce ba su da sauran kwarin gwiwa game da kamfanin TEPCO. Kaza lika rahotanni daga wasu kafofin watsa labarai na nuna cewa, da yawa daga manyan jami’an kasar Japan da suka yi ritaya, suna aiki a kamfanin na TEPCO a matsayin masu ba da shawarwari, kuma wasu jami’ai dake aiki a sashen masana’antun nukiliyar kasar za su shiga gwamnatin ta Japan a matsayin rukunin masu ba da shawara.

Yanzu haka dai watanni biyu ke nan tun bayan da kasar Japan ta fara zubar da ruwan dagwalon nukiliyarta cikin teku. Sai dai abun da ya faru na hadari a baya bayan nan, ya tabbatar da bukatar da ake da ita, ta aiwatar da tsare tsaren sanya ido na kasa da kasa na dogon lokaci, kuma masu inganci.

Idan har da gaske ne kasar Japan tana da karfin gwiwa game da rashin hadarin wannan mataki nata, to kamata ya yi ta zubar da ruwan dagwalon bisa hangen nesa, kana ta goyi bayan kafuwar tsarin sanya ido na dogon lokaci, tare da halartar dukkanin masu ruwa da tsaki, ciki har da sanya ido daga sassa masu zaman kansu daga wasu kasashe.

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Teku dai tamkar gida ne na bai daya ga daukacin bil Adama, kuma bai dace sauran sassan duniya su dauki alhakin son zuciyar kasar Japan ba. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
Next Post
Bashin Biliyan 500 Da Ganduje Ya Bari Ne Ya Hana Mu Fara Aiki Akan Lokaci – Abba

Bashin Biliyan 500 Da Ganduje Ya Bari Ne Ya Hana Mu Fara Aiki Akan Lokaci - Abba

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.