Akalla mutane 15 ne aka ce sun rasu, yayin da wasu uku suka bace bayan da wani kwale-kwale ya kife a kauyen Danmaga da ke karamar hukumar Gummi a jihar Zamfara.
A wani bincike da LEADERSHIP ta gudanar, lamarin ya faru ne a ranar Juma’ar da ta gabata, yayin da wasu mazauna kauye kimanin 20 da suka tsere daga harin ‘yan bindiga suka shiga wani kwale-kwale da ya kife a lokacin da suke kokarin tsallakawa kogi a Nasarawar Kifi da ke unguwar Birnin Tudu.
Majiyoyi sun shaida wa wakilinmu cewa, wadanda lamarin ya rutsa da su, galibinsu mata ne da kananan yara ‘yan kauyen Danmaga da Tungar Maigunya da kuma Nasarawar Kifi da suke neman tsira daga hare-haren ‘yan bindiga inda suka garzaya zuwa bakin kogi domin tsallakawa ta hanyar kwale-kwale.
A cewar majiyar, kwale-kwalen zai iya daukar fasinjoji 16 ne kacal, amma a zagaye na Uku cunkoson matafiyar ya yi yawa inda wasu mata biyu suka tilasta wa kansu afkawa cikin jirgin inda suka zama fasinjoji zuwa 18, ana kyautata zaton cewa, wannan ne ya yi sanadin kifewar kwale-kwalen.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp