• English
  • Business News
Wednesday, September 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Bangaren Tsaro Zai Shimfida Yanayi Mai Kyau Ga Bunkasuwar Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Bangaren Tsaro Zai Shimfida Yanayi Mai Kyau Ga Bunkasuwar Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa kididdgar da aka bayar, yawan nakiyoyin da aka binne a karkashin kasa da suka rage a wurare daban-daban a duniya bayan yake-yake ya kai miliyan 110, lamarin dake zama kalubale ga tsaron duniya. Nahiyar Afirka ma, wuri ne mafi fama da wannan mummunar matsala. An ce, yawan nakiyoyin da aka binne a karkashin kasa da suka rage a kasashen Afirka 19 ya kai kimanin miliyan 37. A kasar Mozambique, rabin nakasassu sun gamu da wannan matsala ne saboda fashewar nakiyoyin. A Angola kuma, ko wani mutum daya cikin mutane 236, ya rasa hannu ko kafa sanadin fashewar nakiyoyin.

 

Ana daukar tsaro da muhimmanci saboda shi ne kashin bayan samun bunkasuwa. Sin ta dade tana dukufa kan taimakawa al’ummar Afirka wajen kawar da nakiyoyin da aka binne a karkashin kasa don tabbatar da jin kai, inda ta dauki matakai na tallafa wa Habasha da Angola da Eritrea da kuma Chadi da sauransu, wajen inganta kwarewarsu ta kawar da nakiyoyin, don kare tsaron jama’ar kasashen da ciyar da bunkasuwar tattalin arziki da zaman al’umma gaba. Sai kuma a gun taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka da ba a dade da rufewa ba a nan birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da aiwatar da aikin taimakawa nahiyar Afirka kawar da nakiyoyin da aka binne a karkashin kasa, don share wannan kablule daga nahiyar.

 

Hadin gwiwa a bangaren tsaro wani muhimmin sashe ne na tabbatar da kyakkyawar makomar Sin da Afirka ta bai daya a ko da yaushe. Sin za ta dukufa kan aiwatar da ayyuka a wannan fanni karkashin tsarin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka, ta yadda za a daga karfin kasashen Afirka na kare zaman lafiya da kwanciyar hankali, da ma shimfida wani yanayi mai kyau ga kasashen wajen tabbatar da tsaro da karko da kuma ci gaba mai dorewa. (Mai zane da rubutu: MINA)

Labarai Masu Nasaba

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Fara Amfani Da Kimiyya Da Fasaha Wajen Yaki Da Cutar Kyandar Biri

Next Post

Za Mu Iya Samar Wa Dubban Matasan Nijeriya Aikin Yi Da Kera Farantin Hasken Rana -Injiniya Abubakar

Related

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

17 hours ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

24 hours ago
Yadda Kasar Sin Ta Nuna Wa Afirka Asalin Ma’Anar Hakkin Dan Adam Sabanin Irin Na Kasashen Yamma
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Nuna Wa Afirka Asalin Ma’Anar Hakkin Dan Adam Sabanin Irin Na Kasashen Yamma

5 days ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

6 days ago
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

1 week ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

1 week ago
Next Post
Za Mu Iya Samar Wa Dubban Matasan Nijeriya Aikin Yi Da Kera Farantin Hasken Rana -Injiniya Abubakar

Za Mu Iya Samar Wa Dubban Matasan Nijeriya Aikin Yi Da Kera Farantin Hasken Rana -Injiniya Abubakar

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

September 3, 2025
Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga Kuɗaɗe – Datti

Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga Kuɗaɗe – Datti

September 3, 2025
Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu

Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu

September 3, 2025
Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci

Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci

September 3, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Ci Yankuna Da Dama A Katsina

Jihohi 18 A Arewa Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Satumba – NiHSA

September 3, 2025
Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

September 3, 2025
Xi Jinping: Tuna Tarihi Da Martaba ’Yan Mazan Jiya Martaba Zaman Lafiya Da Gina Makoma Mai Kyau 

Xi Jinping: Tuna Tarihi Da Martaba ’Yan Mazan Jiya Martaba Zaman Lafiya Da Gina Makoma Mai Kyau 

September 3, 2025
NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su

NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su

September 3, 2025
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

September 3, 2025
Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

September 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.