• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Haifar Da Da Mai Ido

byCMG Hausa
2 years ago
Sin

Yayin da kasashen Afirka ke kara mayar da hankali ga kyautata dangantakarsu da kasar Sin, da ma yadda sassan biyu ke kokarin cika alkawuran da suka yiwa juna, na bunkasa cudanya, da cimma moriya tare, karkashin muhimman shirye-shirye da suka amincewa, muna iya cewa kwalliya tana kara biyan kudin sabulu yadda ya kamata.

Ko da a ranar Alhamis ta makon jiya, mahukuntan kasar Zimbabwe sun kaddamar da aikin fadada tashar lantarki ta Hwange, wadda ke amfani da tururi wajen samar da makamashin lantarki, a yankin Hwange mai nisan kilomita 780 daga birnin Harare, fadar mulkin kasar.

  • Sin Ta Yi Tir Da Umarnin Amurka Kan Sake Bitar Batun Zuba Jari A Kasashen Waje

Kamfanin Sinohydro na kasar Sin ne ya dauki nauyin gudanar da aikin da tallafin gwamnatin kasar Sin, wanda bayan kammala karin manyan injunan sarrafa lantarki 2 a tashar, yanzu haka injunan da tashar ke aiki da su sun kai guda 8, matakin da zai bunkasa yawan lantarkin da kasar za ta rika samu daga wannan tasha, matakin da zai yi tasiri ga raya masana’antun kasar, da fadada guraben ayyukan yi.

Ko shakka babu, kammala wannan muhimmin aiki sakamako ne na hadin gwiwa mai ma’ana tsakanin Sin da Zimbabwe, kamar dai yadda sauran kasashen Afirka ma suke cin gajiya daga makamantan wadannan ayyuka na raya kasa, da more rayuwar al’ummun kasashen.

Masharhanta da dama na jinjinawa kwazon gwamnatin kasar Sin, da sahihiyar aniyar kasar ta tallafawa ayyukan more rayuwa da dama, da take daukar nauyin gudanarwa a Afirka, da ma sauran kasashe masu tasowa a sassan duniya daban daban.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Irin wadannan ayyuka, na shaida kyakkyawan zumunci, da kaunar juna dake tsakanin Sin da kasashen Afirka, yayin da dukkanin sassan biyu ke kara amincewar juna ta fuskar cinikayya, da musayar ilimi da al’adu, da sauran manyan fannonin kyautata rayuwar bil adama, daidai da burin da Sin ta jima tana yayatawa, na tabbatar da gina al’ummar duniya mai makomar bai daya ga daukacin bil adama. (Saminu Hassan)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Fasahar Aikin Gona Da Ire-Iren Hatsi Masu Inganci Na Sin A Bikin Baje Kolin Uganda

Fasahar Aikin Gona Da Ire-Iren Hatsi Masu Inganci Na Sin A Bikin Baje Kolin Uganda

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version