• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hakimi Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Sumbatar Mahaifiyarsa

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Hakimi

Wani abin da ke ci gaba da dauke hankalin mabiya kwallon kafa a gasar cin kofin duniyar da ke gudana a Katar shi ne, yadda dan wasan Morocco, Achraf Hakimi ke rugawa wajen mahaifiyarsa yana sumbatar ta da zaran sun kammala wasa.

Dan wasan kungiyar PSG da ke kasar Faransa na daya daga cikin zaratan ‘yan wasan Morocco da ke ci gaba da samun nasara a wasannin na Katar, ganin yadda suka kawar da manyan kasashe irinsu Spain da Portugal.

  • Qatar 2022: Faransa Ta Doke Morocco A Wasan Zagayen Kusa Da Na Karshe

Hakimi na daga cikin wadanda suka taka gagarumar rawa wajen kai Morocco zuwa matakin wasan kusa da na karshe da suka fafata a ranar Laraba da tawagar Faransa mai rike da kambun gasar.

Sai dai bayan zama daya daga cikin tauraron ‘yan wasan Morocco, Hakimi na dauke hankalin ‘yan kallo da kuma masu bibiyar kasarsa a gasar ta yadda da zarar an kammala wasa ya kan ruga wurin mahaifiyarsa domin sumbatarta a cikin ‘yan kallo.

Yayin da yake tsokaci a kan wannan mataki da yake dauka, Hakimi ya ce iyayensa sun sadaukar da rayukansu wajen taimaka masa zuwa kai wa matakin da yake yanzu, saboda haka ba zai yi watsi da su ba, abin da ya sa yake alfahari da su ko da yaushe.

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Dan wasan ya ce mahaifiyarsa ta yi aikatau a gidajen jama’a domin biya masa bukatu, yayin da mahaifinsa kuma yake sayar da kaya ne a titi domin samar musu abin da za su ci.

Hakimi ya ce wannan sadaukarwar da suka masa wajen aiki tukuru har ya kai shi matakin da yake yanzu ba zai ba shi damar juya musu baya ba, saboda haka yake alfahari da su ko da yaushe.

Ya zuwa wannan lokaci, Hakimi mai shekaru 24 ya yi nasarar buga wasu daga cikin manyan kungiyoyin kasashen Turai irin su PSG da Inter Milan da Borussia da Dortmund, inda ake bayyana shi a matsayin daya daga cikin fitattun ‘yan wasan baya na duniya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0
Wasanni

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane
Wasanni

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni
Wasanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Next Post
Alfanun Da Ke Tattare Da Sabon Tsarin Cire Kudi Na CBN – Sanusi

Alfanun Da Ke Tattare Da Sabon Tsarin Cire Kudi Na CBN – Sanusi

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

Ma’aikatar Wajen Sin Ta Yi Tsokaci Kan Amincewar Da Isra’ila Ta Yi Da Yarjejeniyar Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 10, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho

October 10, 2025
Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

October 10, 2025
peter

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.