• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hakkin Makwabtaka Muhimmin Abu Ne Da Ya Kamata Japan Ta Yi La’akari Da Shi

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Hakkin Makwabtaka Muhimmin Abu Ne Da Ya Kamata Japan Ta Yi La’akari Da Shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin taron hukumar kare hakkin bil adama ta MDD karo 53 dake wakana, kasar Sin ta sake kira ga Japan da ta dakatar da shirinta na zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin teku. Ko a makon da ya gabata, kasar Sin ta yi irin wannan kira, tana cewa bai kamata Japan ta dauki rahoton IAEA a matsayin izini aiwatar da nufin nata ba. 

Ba yanzu kasar Sin da sauran kasashe makwabta suka fara bayyana damuwa dangane da wannan batu ba, lallai ya zama wajibi Japan ta sake nazari game da kudurin nata don ganin ba ta sa son rai a ciki ba. Hakkin makwabtaka babban abu ne, domin a ko da yaushe, makwabta ne ke iya kai dauki na farko-farko idan bukatar hakan ta taso, haka kuma babu wanda zai iya tserewa duk wata annoba da za ta shafi makwabcinsa. Kamata ya yi Japan ta yi nazari, ta kuma duba korafin makwabtanta domin suna da hakki a kanta, kana ta yi la’akari da wasu al’ummominta da su ma suke adawa da matakin nata.

  • Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Yi Yunkurin Amfani Da Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku

Idan Japan ta yi gaban kanta tare da biyewa kasashe masu hure mata kunne, lallai mummunan tasirin abun da za ta aiwatar ba zai tsaya kan makwabtanta ba, ita kanta za ta dandana kudarta, don haka, gudun kar a yi, to kar ma a fara.

Kamar yadda kasar Sin ta bayyana, bai kamata Japan ta dauki rahoton da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya (IAEA) ta fitar a matsayin izinin zubar da dagwalon nukiliya cikin tekun ba, domin alamomi sun nuna cewa, an yi gaggawar fitar da rahoton, kana ba a sanar da dukkanin masanan da suka yi nazarin sakamakon ba. Ko kadan gaggauta fitar da rahoto game da muhimmin batu irin wannan bai dace ba, kuma ba zai haifar da da mai ido ba, domin akwai abubuwa da dama da ya kamata a yi la’akari da su duba da cewa, ya shafi al’ummomi da dama.

Abu mafi dacewa shi ne, Japan ta dakatar da shirin, ta hada kai tare da tuntubar masana daga kasashen makwabtanta da ma hukumar IAEA, domin sake gudanar da nazari wanda zai kasance bisa gaskiya da adalci da ilimi, su daddale, su lalubo mafita mafi dacewa da za ta karbu ga dukkan bangarori, ba tare da cutar da wani ba, haka kuma wadda za ta dore. Kana, Japan ta daina sauraron zugar kasashen yamma wadanda kansu kadai suka sani, kana ba su da masaniya ko ma ba su damu da yanayin da shirin zai iya jefa al’ummar yankin ba. (Fa’iza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Nemi Majalisa Ta Tabbatar Da Nadin Sabbin Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Next Post

Bayan Sati 6 Da Barin Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa, Osinbajo Ya Samu Sabon Mukami

Related

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya
Daga Birnin Sin

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

3 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

5 hours ago
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

6 hours ago
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

7 hours ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

24 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

1 day ago
Next Post
An Yi Wa Mataimakin Shugaban Nijeriya Osinbajo Tiyata A Kafarsa

Bayan Sati 6 Da Barin Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa, Osinbajo Ya Samu Sabon Mukami

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.