• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hakkin Makwabtaka Muhimmin Abu Ne Da Ya Kamata Japan Ta Yi La’akari Da Shi

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Hakkin Makwabtaka Muhimmin Abu Ne Da Ya Kamata Japan Ta Yi La’akari Da Shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin taron hukumar kare hakkin bil adama ta MDD karo 53 dake wakana, kasar Sin ta sake kira ga Japan da ta dakatar da shirinta na zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin teku. Ko a makon da ya gabata, kasar Sin ta yi irin wannan kira, tana cewa bai kamata Japan ta dauki rahoton IAEA a matsayin izini aiwatar da nufin nata ba. 

Ba yanzu kasar Sin da sauran kasashe makwabta suka fara bayyana damuwa dangane da wannan batu ba, lallai ya zama wajibi Japan ta sake nazari game da kudurin nata don ganin ba ta sa son rai a ciki ba. Hakkin makwabtaka babban abu ne, domin a ko da yaushe, makwabta ne ke iya kai dauki na farko-farko idan bukatar hakan ta taso, haka kuma babu wanda zai iya tserewa duk wata annoba da za ta shafi makwabcinsa. Kamata ya yi Japan ta yi nazari, ta kuma duba korafin makwabtanta domin suna da hakki a kanta, kana ta yi la’akari da wasu al’ummominta da su ma suke adawa da matakin nata.

  • Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Yi Yunkurin Amfani Da Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku

Idan Japan ta yi gaban kanta tare da biyewa kasashe masu hure mata kunne, lallai mummunan tasirin abun da za ta aiwatar ba zai tsaya kan makwabtanta ba, ita kanta za ta dandana kudarta, don haka, gudun kar a yi, to kar ma a fara.

Kamar yadda kasar Sin ta bayyana, bai kamata Japan ta dauki rahoton da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya (IAEA) ta fitar a matsayin izinin zubar da dagwalon nukiliya cikin tekun ba, domin alamomi sun nuna cewa, an yi gaggawar fitar da rahoton, kana ba a sanar da dukkanin masanan da suka yi nazarin sakamakon ba. Ko kadan gaggauta fitar da rahoto game da muhimmin batu irin wannan bai dace ba, kuma ba zai haifar da da mai ido ba, domin akwai abubuwa da dama da ya kamata a yi la’akari da su duba da cewa, ya shafi al’ummomi da dama.

Abu mafi dacewa shi ne, Japan ta dakatar da shirin, ta hada kai tare da tuntubar masana daga kasashen makwabtanta da ma hukumar IAEA, domin sake gudanar da nazari wanda zai kasance bisa gaskiya da adalci da ilimi, su daddale, su lalubo mafita mafi dacewa da za ta karbu ga dukkan bangarori, ba tare da cutar da wani ba, haka kuma wadda za ta dore. Kana, Japan ta daina sauraron zugar kasashen yamma wadanda kansu kadai suka sani, kana ba su da masaniya ko ma ba su damu da yanayin da shirin zai iya jefa al’ummar yankin ba. (Fa’iza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Nemi Majalisa Ta Tabbatar Da Nadin Sabbin Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Next Post

Bayan Sati 6 Da Barin Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa, Osinbajo Ya Samu Sabon Mukami

Related

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

17 hours ago
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

18 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

19 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

20 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

21 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

2 days ago
Next Post
An Yi Wa Mataimakin Shugaban Nijeriya Osinbajo Tiyata A Kafarsa

Bayan Sati 6 Da Barin Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa, Osinbajo Ya Samu Sabon Mukami

LABARAI MASU NASABA

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.