• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hakkin Makwabtaka Muhimmin Abu Ne Da Ya Kamata Japan Ta Yi La’akari Da Shi

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Hakkin Makwabtaka Muhimmin Abu Ne Da Ya Kamata Japan Ta Yi La’akari Da Shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin taron hukumar kare hakkin bil adama ta MDD karo 53 dake wakana, kasar Sin ta sake kira ga Japan da ta dakatar da shirinta na zubar da ruwan dagwalon nukiliya a cikin teku. Ko a makon da ya gabata, kasar Sin ta yi irin wannan kira, tana cewa bai kamata Japan ta dauki rahoton IAEA a matsayin izini aiwatar da nufin nata ba. 

Ba yanzu kasar Sin da sauran kasashe makwabta suka fara bayyana damuwa dangane da wannan batu ba, lallai ya zama wajibi Japan ta sake nazari game da kudurin nata don ganin ba ta sa son rai a ciki ba. Hakkin makwabtaka babban abu ne, domin a ko da yaushe, makwabta ne ke iya kai dauki na farko-farko idan bukatar hakan ta taso, haka kuma babu wanda zai iya tserewa duk wata annoba da za ta shafi makwabcinsa. Kamata ya yi Japan ta yi nazari, ta kuma duba korafin makwabtanta domin suna da hakki a kanta, kana ta yi la’akari da wasu al’ummominta da su ma suke adawa da matakin nata.

  • Sin Ta Bukaci Japan Da Kada Ta Yi Yunkurin Amfani Da Rahoton IAEA A Matsayin Izinin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku

Idan Japan ta yi gaban kanta tare da biyewa kasashe masu hure mata kunne, lallai mummunan tasirin abun da za ta aiwatar ba zai tsaya kan makwabtanta ba, ita kanta za ta dandana kudarta, don haka, gudun kar a yi, to kar ma a fara.

Kamar yadda kasar Sin ta bayyana, bai kamata Japan ta dauki rahoton da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya (IAEA) ta fitar a matsayin izinin zubar da dagwalon nukiliya cikin tekun ba, domin alamomi sun nuna cewa, an yi gaggawar fitar da rahoton, kana ba a sanar da dukkanin masanan da suka yi nazarin sakamakon ba. Ko kadan gaggauta fitar da rahoto game da muhimmin batu irin wannan bai dace ba, kuma ba zai haifar da da mai ido ba, domin akwai abubuwa da dama da ya kamata a yi la’akari da su duba da cewa, ya shafi al’ummomi da dama.

Abu mafi dacewa shi ne, Japan ta dakatar da shirin, ta hada kai tare da tuntubar masana daga kasashen makwabtanta da ma hukumar IAEA, domin sake gudanar da nazari wanda zai kasance bisa gaskiya da adalci da ilimi, su daddale, su lalubo mafita mafi dacewa da za ta karbu ga dukkan bangarori, ba tare da cutar da wani ba, haka kuma wadda za ta dore. Kana, Japan ta daina sauraron zugar kasashen yamma wadanda kansu kadai suka sani, kana ba su da masaniya ko ma ba su damu da yanayin da shirin zai iya jefa al’ummar yankin ba. (Fa’iza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Nemi Majalisa Ta Tabbatar Da Nadin Sabbin Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Next Post

Bayan Sati 6 Da Barin Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa, Osinbajo Ya Samu Sabon Mukami

Related

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

13 hours ago
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala
Daga Birnin Sin

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

15 hours ago
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

17 hours ago
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

18 hours ago
Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Bayan Taron Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

20 hours ago
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Matakan Cimma Nasarar Sassan Tsaron Kasa

20 hours ago
Next Post
An Yi Wa Mataimakin Shugaban Nijeriya Osinbajo Tiyata A Kafarsa

Bayan Sati 6 Da Barin Ofishin Mataimakin Shugaban Kasa, Osinbajo Ya Samu Sabon Mukami

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

May 13, 2025
Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

May 13, 2025
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

May 13, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

Mahaifin Tsohon Gwamnan Kaduna, Ramalan Yero, Ya Rasu

May 13, 2025
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

May 12, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe

May 12, 2025
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

May 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.