• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hannu Daya Ba Ya Daukar Jinka: Gudummawar Kamfanonin Sin A Fannin Raya Hulda Da Kasashen Afirka

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Hannu Daya Ba Ya Daukar Jinka: Gudummawar Kamfanonin Sin A Fannin Raya Hulda Da Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar dai yadda gwamnatin kasar Sin ta jima tana alkawarta burinta na bunkasa hadin gwiwa da kasashe kawayenta na nahiyar Afirka, ta hanyar bunkasa kawance, da tallafa musu ta dukkanin hanyoyin da suka dace, ta yadda hakan zai ba da damar kaiwa ga kafa alummar Sin da Afirka mai makomar bai daya, kamfanonin kasar Sin a nasu bangaren na yin duk mai yiwuwa, wajen ganin an cimma wadannan manufofi, inda a kasashen Afirka daban daban, ake ganin yadda kamfanonin na Sin dake ayyuka a can, suke zurfafa ayyukan inganta musaya, da ba da tallafi ga alummun wurin.

Ga misali a baya bayan nan, wani rahoton bincike da aka fitar a kasar Uganda, ya nuna yadda kamfanonin Sin ke dora muhimmancin gaske kan yaukaka kawance tsakanin su da alummun kasar, ta hanyar gudanar da ayyukan raya alumma, da kyautata zamantakewa.

  • Wang Yi Ya Jagoranci Taron Manyan Wakilai Game Da Nazarin Matakan Aiwatar Da Manufofin Taron Ministocin FOCAC Na 8

Rahoton mai taken “Rahoton shekarar 2022 game da sauke nauyin tallafawa alumma da kamfanonin kasar Sin ke gudanarwa”, ya nuna yadda kamfanonin na Sin ke taimakawa alummun wuraren da suke gudanar da ayyukansu da kayayyakin kiwon lafiya, da na yaki da cututtuka, da na tallafin karatu, da horon samun kwarewar sanaoi da sanin makamar aiki, da ayyukan gyaran makarantu da dai sauran su.

Ko shakka babu, irin wadannan manufofi da matakai da kamfanonin kasar Sin dake kasashen Afirka ke aiwatarwa, suna taka rawar gani wajen ingiza ci gaban kasashen nahiyar, kamar yadda ake gani yanzu haka a Uganda, inda tuni irin wadannan ayyuka suka tallafa a fannonin raya harkokin sufuri, da makamashi, da gina ababen more rayuwar alumma.

A hannu guda, mahukuntan kasar Sin na kara jaddada aniyarsu ta cika alkawuran da tka dauka, na gudanar da manyan manufofin nan gudan takwas, wadanda Sin ta gabatar yayin taron dandalin ministocin Sin da na kasashen Afirka karo takwas, karkashin dandalin bunkasa hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka na FOCAC, wanda ya gudana a shekarar bara a kasar Senegal, inda karkashin manufofin ake sa ran nahiyar Afirka za ta ci karin gajiya mai yawa daga kasar Sin, a fannonin samar da ababen more rayuwar jamaa daga dukkanin fannoni.

Labarai Masu Nasaba

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu-Yanzu: Kotu Ta Tabbatar Da Mohammed Abacha A Matsayin Da Takarar Gwamnan PDP A Kano

Next Post

An Kammala Kashin Farko Na Layin Dogon Jihar Lagos

Related

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya
Daga Birnin Sin

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

16 hours ago
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

17 hours ago
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

18 hours ago
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

19 hours ago
Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

20 hours ago
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa
Daga Birnin Sin

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

2 days ago
Next Post
An Kammala Kashin Farko Na Layin Dogon Jihar Lagos

An Kammala Kashin Farko Na Layin Dogon Jihar Lagos

LABARAI MASU NASABA

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.