• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hannu Daya Ba Ya Daukar Jinka: Gudummawar Kamfanonin Sin A Fannin Raya Hulda Da Kasashen Afirka

by CMG Hausa
3 years ago
Afirka

Kamar dai yadda gwamnatin kasar Sin ta jima tana alkawarta burinta na bunkasa hadin gwiwa da kasashe kawayenta na nahiyar Afirka, ta hanyar bunkasa kawance, da tallafa musu ta dukkanin hanyoyin da suka dace, ta yadda hakan zai ba da damar kaiwa ga kafa alummar Sin da Afirka mai makomar bai daya, kamfanonin kasar Sin a nasu bangaren na yin duk mai yiwuwa, wajen ganin an cimma wadannan manufofi, inda a kasashen Afirka daban daban, ake ganin yadda kamfanonin na Sin dake ayyuka a can, suke zurfafa ayyukan inganta musaya, da ba da tallafi ga alummun wurin.

Ga misali a baya bayan nan, wani rahoton bincike da aka fitar a kasar Uganda, ya nuna yadda kamfanonin Sin ke dora muhimmancin gaske kan yaukaka kawance tsakanin su da alummun kasar, ta hanyar gudanar da ayyukan raya alumma, da kyautata zamantakewa.

  • Wang Yi Ya Jagoranci Taron Manyan Wakilai Game Da Nazarin Matakan Aiwatar Da Manufofin Taron Ministocin FOCAC Na 8

Rahoton mai taken “Rahoton shekarar 2022 game da sauke nauyin tallafawa alumma da kamfanonin kasar Sin ke gudanarwa”, ya nuna yadda kamfanonin na Sin ke taimakawa alummun wuraren da suke gudanar da ayyukansu da kayayyakin kiwon lafiya, da na yaki da cututtuka, da na tallafin karatu, da horon samun kwarewar sanaoi da sanin makamar aiki, da ayyukan gyaran makarantu da dai sauran su.

Ko shakka babu, irin wadannan manufofi da matakai da kamfanonin kasar Sin dake kasashen Afirka ke aiwatarwa, suna taka rawar gani wajen ingiza ci gaban kasashen nahiyar, kamar yadda ake gani yanzu haka a Uganda, inda tuni irin wadannan ayyuka suka tallafa a fannonin raya harkokin sufuri, da makamashi, da gina ababen more rayuwar alumma.

A hannu guda, mahukuntan kasar Sin na kara jaddada aniyarsu ta cika alkawuran da tka dauka, na gudanar da manyan manufofin nan gudan takwas, wadanda Sin ta gabatar yayin taron dandalin ministocin Sin da na kasashen Afirka karo takwas, karkashin dandalin bunkasa hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka na FOCAC, wanda ya gudana a shekarar bara a kasar Senegal, inda karkashin manufofin ake sa ran nahiyar Afirka za ta ci karin gajiya mai yawa daga kasar Sin, a fannonin samar da ababen more rayuwar jamaa daga dukkanin fannoni.

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani
Daga Birnin Sin

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 
Daga Birnin Sin

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Next Post
An Kammala Kashin Farko Na Layin Dogon Jihar Lagos

An Kammala Kashin Farko Na Layin Dogon Jihar Lagos

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Asuu

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.