• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Tukunyar Rikicin Masarautar Kano Na Tafarfasa

by Sulaiman and Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
Kano

Duk da sa bakin wasu da ake kallo a matsayin wadanda karansu ya kai tsaiko, ku-ma ake da kyakkyawan zaton idan suka ce ga yadda za a yi, to za a yi wa tufkar hanci, amma dai har yanzu kura tukunyar rikicin masarautun Kano na ci gaba da kara tafasa.

Wannan shi ne irinsa na farko a tarihin masarautar Kano, masu sarhi sun hakikance cewar siyasa ce ke zaman musabbabin wannan danbarwa. Wanda kuma idan ba a yi wa tufkar hanci ba, za ta iya zama wata gobara daga teku. Mu-samman Ganin yadda lamarin ya fara yaduwa zuwa wasu masarautun wadan-da zuwa yanzu aka jin yadda aka fara yamutsa gashin baki.

  • Ganduje Da Mai Dakinsa Za Su Gurfana A Gaban Kotu A Kano
  • Matsalar Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Sanya Dokar Takaita Zirga-zirgar Ababen Hawa

Yanzu haka an fara jin motsin irin wannan matsalar ta fara fitowa a wasu jihohi biyu na arewacin kasar nan, wanda suka hada da Sakwato da Katsina. A Jihar Sakwato har an kai irin wannan kudiri gaban majalisar dokokin jihar, inda ake za-ton irin wannan guguwar na neman yin awon gaba da rawanin Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar. Yayin da a Jihar Katsina kuwa, shi ma Mai Martaba Sarkin Kataina, ya karbi takardar da ke neman ya yi bayanin dalilinsa na kin yin hawan sallar da ta gabata.

Yanzu haka lamarin kullum daukar sabon salo yake a Masarautar ta Kano, domin kamar yadda aka sani sarakuna biyu ke mulki a Kano, guda ya samu rakiya tare da kariyar gwamna, wanda aka shigar da shi gidan Rumfa cikin dare, yayin da daya bangaren kuma yake gudanar da mulki daga gidan Nassarawa, wurin da ke samun tsaro daga jami’an ‘yansanda da sojoji.

A bangaren rundunar ‘yansanda kuwa, ta shelanata yin tsayuwar daka kancewar tana bin umarnin kotu ne, don haka take bayar da kariya ga Sarki Aminu Ado Bayero, inda wata kotu ta dakatar da Gwamnan Abba Kabir Yusuf daga ci gaba da daukar kowane irin mataki a kansa har sai ta kammala shari’ar da ke gabanta.

LABARAI MASU NASABA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

Sai dai kuma gwamna ya sa kafa ya yi fatali da umarnin na kotun, ya rattaba wa dokar hannu da aka yi wa kwaskwarima tare da damka wa Muhammadu Sanusi II takarda sake dawo da shi a matsayin sarkin Kano na 16.

Haka zalika, ana ta samun mabanbantan tunani, inda wasu ke tururuwar zuwa fadar gidan Runfa domin yin mubayi’a ga Sarki na 16, Muhammadu Sanusi II, mu-samman jami’an gwamnati da masu biyayya ga darikar kwankwasiyya, wannan tasa wata kididdiga ta nuna cewa Sarkin Kano na 16 ya karbi mubayi’ar hakimai sama da guda 40, wanda kuma wannan kamar yadda wata majiya ta tsegunta wa wakilinmu na samun umarnin zuwa mubayi’ar ne daga fadar gwamnati, kuma suna zuwa domin gudun asarar rawaninsu.

Kamar yadda aka sani akwai kararraki har guda uku da ke gaban kotuna, inda wa-ta kotun tuni ta yi fatali da nade-naden da gwamna ya yi ta kuma tabbatar da ce-wa, Aminu Ado ne halastaccen Sarki. Bayan yanke wannan hukunci ne kotun ta mika wa kotun da bangaren gwamnati ta daukaka kara domin ci gaba da shari’ar. Haka kuma akwai kotun da tuni ta yanke hukunci tare da cin tarar gwamnatin Ka-no har naira miliyon 10.

Sannan akwai kotun da gwamnatin Kano tare da majalisar dokokin Jihar Kano su-ka kai kara, inda kotun ta ba da umarnin lallai a fitar Sarki Aminu Ado Bayero daga gidan Nassarawa. Wannan kotun na karkashin Mai Shari’a Amina Adamu Aliyu.

A cikin makon da ya gabata ne kuma aka wayi gari da ganin an tayar da tuta a gidan Sarki Nassarawa, wanda hakan wata shaida ce da ke nuna cewa sarki na nan, kuma bisa muhimmancin wannan tuta wadda ita ce shaidar tutar da Shehu Usman Danfodio ya raba wa sarakunan Musulunci.

A martanin daya bangaren ta bakin shugaban jam’iyyar NNPP, Alhaji Hashimu Dugurawa ya bayyana cewa wannan tuta ba ta wuce kokarin da wani ke yi na ku-la da makabartar da ake bizne iyayensu a ciki ba.

Dugurawa ya ce wadancan sarakuna biyar ba su da maraba da kwamishinoni, domin an nada su ne saboda su taimaka wa Ganduje cin zabe, kuma ya fadi, don haka a cewarsa ya yi mamakin da tuni ma ba su sauka daga kujerun da suke kai ba kasancewar shi ma Ganduje ya bar tasa kujerar.

Yanzu haka dai an samu matsayar kutna biyu cikin ukun da ke gaban alkalai, inda kutuna biyu suka zantar da hukuncin da ke nuni ga halascin Sarkin Aminu Ado Bayero, duk da cewa kotun gwmanatin ta yanke hukunci ne kan nade-naden da Ganaduje ya aiwatar bayan samun umarnin kotu na tsaya wuri guda har zuwa lo-kacin da kotun za ta kammala sauraron korafin da aka gabatar mata.

Gwamna Abba ya yi tali da umarnin na kotu duk irin kallon da duniya ke masa na cewa shi kansa ribar hukuncin kotuna yake ci, domin da kotu ba ta ba shi nasara a shari’ar da kowa ya yanke tsammanin samun nasarar jam’iyyar NNPP ba, sakamakon hukuncin kwace kujerar har karo biyu da kotun farko da ta biyu suka yi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu
Labarai

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe
Labarai

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Next Post
Cika Shekara 100 A Duniya: Tarihin Shaikh Dahiru Bauchi Daga Bakinsa

Cika Shekara 100 A Duniya: Tarihin Shaikh Dahiru Bauchi Daga Bakinsa

LABARAI MASU NASABA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.