• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harin Da Amurka Ta Kaiwa Iraki Babban laifi Ne

by CMG Hausa
3 years ago
Iraki

A bana ne ake cika shekaru 20, tun bayan da Amurka ta kaddamar da kai yaki a kasar Iraki. Wani nazarin jin ra’ayin jama’ar duniya da kafar CGTN ta gudanar, ya nuna cewa kaso 93.15 cikin 100 cikin mutanen da suka bayyana ra’ayinsu game da wannan yaki, sun nuna cewa, ya kamata Amurka ta dauki alhakin aiwatar da laifin yaki a Iraki.

A cikin shekaru 20 din da suka gabata, Amurka da kawayenta, sun kaiwa Iraki hari ba tare da samun izini daga MMD ba, bisa hujjar cewa, wani ta gano makaman kare-dangi a kasar Iraki. Amma daga baya, an tabbatar da cewa, Iraki ba ta da irin wadannan makamai. Wannan ya kara tabbatar da zalunci da nuna fin karfi na Amurka kan wasu kasashe.

  • CMG Ya Rattaba Hannu Kan Takardar Tunatarwar Hadin Gwiwa Da Jaridar Rasha

Bayanai na nuna cewa, kaso 94.6 cikin 100 na yawan mutanen da aka ji ra’ayinsu na ganin cewa, babu wani dalilin da zai sa Amurka ta kaddamar da wannan yaki a Iraki, kuma yin hakan laifi ne.

A cikin wadannan shekaru 20 da suka gabata, yawan fararen hula da suka mutu, ko suka jikkata, ya kai fiye da dubu 200, yayin da wasu miliyoyin mutane suka rasa gidajensu. A nasu bangare kuwa, sojojin Amurka 4,572 sun mutu, kana yawan kudin da kasar ta kashe ya kai fiye da dala triliyan 2. Abin da duniya take bukata, shi ne zaman lafiya ba yaki ba.

A yayin da aka cika shekaru 20 da kaddamar da haramtaccen yakin Iraki, wajibi ne wasu ’yan siyasa na Amurka sun sake tunani don dakatar da ta da zaune tsaye a sauran wurare da sunan demokuradiyya, bai dace Amurka ta rika tilastawa kasashe bin tsarin demokiradiyarta ba. Ya kamata kasashe su zabi tsarin demokiradiya da ma na bunkasuwa da ya dace da yanayin kasashensu.

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

Masu sharhi na cewa, ko shakka babu harin da gwamnatin Amurka ta kaiwa Iraki da ma wasu kasashe a sassan duniya da sunan demokiradiya ko kare wani nau’i na muradunta, babban laifi ne. Kowane tsuntsun kukan gidansu yake yi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin
Daga Birnin Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Next Post
Tinubu Ya Tafi Faransa Hutu, Zai Ziyarci Saudiyya  Don Yin Dawafi

Tinubu Ya Tafi Faransa Hutu, Zai Ziyarci Saudiyya Don Yin Dawafi

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

November 8, 2025
Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Yadda Ake Miyar Margi

Yadda Ake Miyar Margi

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.