• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Harkar Waka Da Fim Na Bukatar Tallafin Gwamnati Don Bunkasa -Okasha Ibrahim Mu’azu

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
in Nishadi
0
Harkar Waka Da Fim Na Bukatar Tallafin Gwamnati Don Bunkasa -Okasha Ibrahim Mu’azu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daya daga cikin mawakan da ke tasowa a yanzu cikin masana’antar Kannywood, OKASHA IBRAHIM MU’AZU Wanda aka fi sani da OKA DAN ALHAJI. Ya bayyana wa masu karatu irin kalubalen da ya fuskanta bayan ya fara waka tare da irin burikan da ya ke da su game da waka, har ma da sauran batutuwan da suka shafi sana’arsa ta waka. Ga dai tattaunawar tare da LUBABATU AUTA INGAWA Kamar haka:

Da farko masu karatu za su so su ji cikakken sunanka, tare da takaitaccen tarihinka

Da farko dai sunana Okasha Ibrahim Mu’azu, wanda aka fi sani da Oka Dan Alhaji mawaki a msana’antar Kannywood. An haife ni a Jihar Katsina a karamar hukumar Bakori, a wani kauye mai suna unguwar Shantali. Na yi karatun firamare a cikin gari unguwar Shantali, nayi Sakandare a cikin garin Bakori.

 

Za ka kai kamar shekara nawa da fara waka?

Labarai Masu Nasaba

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Na fara waka a shekara ta dubu biyu da sha takwas wato 2018.

 

Ya ka dauki waka a wajenka?

A gaskiya ni na dauki waka a matsayin sana’a.

 

Ya gwagwarmayar shiga masana’antar ya kasance?

Gaskiya kuwa na sha kalubale daban-daban, musamman alakar mu da mutane ta yadda wasu suke kallonmu a marasa tarbiyya, musamman na jikiinmu

Waka

Idan na fahimce ka daga Iyaye, ‘yan uwa da abokai ka samu wani sauyi na zamantakewa da suka yi sanadiyar fara waka?

A gaskiya ni ban samu wata damuwa daga iyayena ba, kasancewata mawaki, amma a cikin ‘family’ dinmu na fuskanci kananun maganganmu wanda ya sa har yanzu ana ganin aikin banza nake yi, wasu ma daga cikinsu suna ganin shurme na kawai nake yi.

 

A ganinka wanne dalili ne ya sa har yanzu suke kallon shirme ka ke yi, Baka samu wani canjin rayuwa bane tun da ka fara wakar ko kuwa akwai abin da ka ke yi na kasuwanci ko karatu, amma ka daina yinsu silar wakar da suke yi maka kananun maganganu?

Su kansu yanzu haka lokaci ya fara nuna masu cewar wakar da nake yi ba shirme bace ba, tunda har sun fara jin nasu ne musamman idan suka yi nisa da gida su ji yankin suna sauraren wakokina. Maganar karatu kuma ko kasuwanci duk ba daya daga ciki da za su yi tunanin waka za ta hana ni gudanar da su, kuma koda su basu sani ba wasu sunan cewa kasuwanci ai shi ne jigon karamin mawaki.

 

Da wacce waka ka fara ya karbuwar wakar ta kasance ga su masu saurara?

Eh! wakata ta farko ita ce; Wakar Zainab kuma Alhamdulillah lokacin da na yi wakar wasu ma cewa suke wai ba ni na yi ta ba, saboda mamakin da sukai ace wai yau Oka ne yake waka abin ya basu mamaki sosai fa, daga nan kuma sai mutanen garinmu suka yi tayin tururuwa zuwa wajena domin na tura masu wakata.

 

Sunan wakarka ta farko Zainab. Akwai wata Zainab da ka ke da alaka da ita ne wadda dalilinta ya sa kayi wakar ko kuwa ya abin ya ke?

Eh! gaskiya a wannan lokacin ina tare da Zainab sakamakon haka ne ma ya sa nayi wa Zainab waka.

 

Zainab din ‘yar uwa ce ko Budurwa, Ya ya alakarka take da ita da kuma bayan ka fara wakar?

Abu ne ya zama guda biyu a lokacin wanda har kawo iyanzu wasu na yin maganganu, sakamakon rabuwata da wata ‘yar uwa mai suna Zainab, wadda a lokacin iyayenmu suka so na aureta har baiko da sa rana aka yi amin da ita, to bayan munrabu da ita kuma sai na fara soyayya da wannan zainab din da nayi wa waka.

Waka

Kana da ubangida a cikin masana’antarku?

Gaskiya ba ni da ubangida a harkar waka

 

Da wanne mawaki ko mawaki ka fi so kayi waka?

Eh! gaskiya ina son yin waka da Fati Niger sannan kuma ina son yin waka da Hamisu Breaker ko dan masoyanmu, sakamakon dubban mutane suna ganin kamannin da muke yi wasu ma suna tunanin ni da shi ‘yan uwa ne.

 

Mene ne yake birgeka a cikin wakokin Hamisu Breaker da na Fati Niger wanda har ya ja hankalinka ka ke son yin waka da su?

Gaskiya Fati Niger mawakiya ce wadda na dade ina jin wakokinta muryarta ta fita daban a cikin mata mawaka, shiyasa nake son na yi waka da ita, sakamakon duk wanda ya ji ya san ita ce, shi kuma Hamisu ta yadda salonmu ya zo daya da har ya sa idan nayi hoto ko bideo masoyansa suke bibiyata da son ganina a koda yaushe. Sannan kuma a cikin gidan mu ko iyayena idan za su yi magana akan Hamisu sai su musaltashi da ni, hakan ya sa na ji ina son yin waka da shi, sannan kuma masoyanmu suma suna bukatar hakan.

 

Bayan waka kana yin fim ne, ko kana sha’awar shiga fim?

Gaskiya bana yin fim kuma bana sha’awar yin fim.

 

Mene ne burinka na gaba game da waka?

Ina son a duk inda na shiga a ce Oka Dan Alhaji, kuma ina son na daukaka a harkar waka idan Allah ya sa ina daga cikin masu daukaka.

 

Wacce irin mace ka ke son aura?

Ina son mace wadda ta san darajar kanta kuma ta san darajar dan Adam.

 

Wanne irin abinci da abun sha ka fi so?

Abinci ina son Dan Wake sosai, abun sha kuma ina son Multina sosai.

 

Ya alakarka da sauran abokan aikinka?

Muna zaune lafiya da ganin mutuncin juna, muna rayuwa cikin aminci da kulawar junanmu.

 

Wacce shawara za ka bawa masu kokarin shiga masana’antar dan fara waka?

Eh! to ga dukkanin mai son ya shiga wannan masana’antar to gaskiya abu biyu ne zuwa uku na farko yaddar iyaye, na biyu hakuri na uku tsabtace harshenka zuwa zuciyarka.

 

Me za ka ce ga masu yi wa mawaka mummuna kallo?

Su ji tsoron Allah kuma kafin su yi zagi a gare mu su fara duba nasu laifin, sannan sai su yi wa kansu hukunci domin mawaki ko dan fim ba hakan yana nufin cewa sun kauce hanya bane, kowacce irin sana’a tanada wuta kuma tanada aljanna kuma ko kai malami ne ko sabanin hakan.

 

Ko akwai wani kira da za ka yi ga gwamnati game da ci gaban mawaka?

Gaskiya ne yanada kyau gwamnati ta san cewa a harkar waka ko fim muna bukatar tallafi da kuma nuna amincinta a cikin harkar, saboda muma muna son ci gaban da sauran kasashe suka samu daga wannan masana’anta, ina mai jan hankalin gwamnati da ta kara inganta harkar ko dan samun ci gaban kasata.

 

Me za ka ce ga makaranta shafin Rumbun Nishadi?

Ina yi masu fatan alkairi kuma da sakon gaisuwa a gare su, sannan ga dukkanin me bukatar wakokina ya biyoni ta audiomack mai suna [email protected] ko Oka Dan Alhaji TB, na gode sosai.

 

Me za ka ce da ita kanta Jaridar Leadership Hausa?

Wannan jarida ina matukar godiya a gare ku, kuma ina rokon Allah ya kara daukaka ta Allah ya taimaka, sannan wannan shirye-shiryen da ku ke yi Allah ya kara dankon zumunci.

 

Amin summa amin muna godiya da wannan addu’a, Ko kana da wadanda za ka gaisar?

Ina gaida Aunty aisha wadda ta hada ni da ku, ina yi mata fatan alkairi. Sannan ina mika gaisuwa ga Bilkisu wadda bana ce komai a kanta ba, sannan ina gaida dukkanin masoyana dake fadin duniya baki daya.

 

Muna godiya da kasancewa tare da mu daga farko har izuwa karshen wannan Tattaunawa.

Ni ma na gode sosai da kasancewar da ku ka yi tare da ni domin tattaunawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Fina-FinaiKannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Tare Da Sabuwar Gwamnatin Zimbabwe

Next Post

Bankin Samar Da Ci Gaba Na Sin Da Bankin Shige Da Fice Na Afirka Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Rancen Kudi

Related

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa
Nishadi

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

3 days ago
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa
Nishadi

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

2 weeks ago
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau
Nishadi

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

3 weeks ago
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

3 weeks ago
Babu Irin ArziÆ™in Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
Nishadi

Babu Irin ArziÆ™in Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

1 month ago
Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)
Nishadi

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

1 month ago
Next Post
Bankin Samar Da Ci Gaba Na Sin Da Bankin Shige Da Fice Na Afirka Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Rancen Kudi

Bankin Samar Da Ci Gaba Na Sin Da Bankin Shige Da Fice Na Afirka Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Rancen Kudi

LABARAI MASU NASABA

Babu Wata Karamar Hukumar Dake ƘarÆ™ashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Dake ƘarÆ™ashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

July 29, 2025
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

July 29, 2025
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

July 29, 2025
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

July 29, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.