• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hisbah Ta Ceto Ƴanmata 16 Daga Hannun Masu Safarar Mutane A Kano

by Salim Sani Shehu
6 months ago
in Labarai
0
Hisbah Ta Ceto Ƴanmata 16 Daga Hannun Masu Safarar Mutane A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an hukumar Hisbah ta jihar Kano sun yi nasarar kuɓutar da wasu ‘yan mata 16 daga hannun wasu da ake zargin masu safarar mutane ne a tashar motar da ke Unguwa Uku a Kano.

Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda lamarin ya rutsa da su ƙananan yara kan hanyarsu ta zuwa Legas, inda za a yi safarar su zuwa Jamhuriyar Benin da Ghana.

  • Hisbah Ta Yi Kakkausan Gargaɗi Tare Da Kira Ga Iyaye Kan Kula Da Yara Bayan Samun Gawar Wasu 4
  • Kwankwaso Ya Soki Ƴansandan Kano, Ya Buƙaci A Girmama Ƴancin Kano

Da yake jawabi mataimakin kwamandan Hisbah, Mujahid Aminuddeen Abubakar, ya ce, “Jami’an mu a tashar mota sun kama wasu mutane da suke yunkurin safarar waɗannan ‘yan mata masu ƙarancin shekaru. Wasu za su iya rasa rayukansu, yayin da wasu za a sayar da su, a tilasta musu yin karuwanci, ko kuma a bautar da su”

Abubakar ya bayyana cewa ‘yan matan da aka ceto ba su da masaniya kan illolin da za su fuskanta. Dukkansu sun fito daga ne arewacin Nijeriya, daga jihohin Kano da Katsina da Jigawa, da kuma jihar Borno.

Ya kuma buƙaci iyaye da su kara taka tsan-tsan tare da ba da fifiko ga tsaron ‘ya’yansu, yana mai gargadin kada su jefa su cikin irin wannan haɗari domin samun kuɗi.

Labarai Masu Nasaba

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

“Dole ne iyaye su ɗauki nauyi kuma su kare ’ya’yansu. Yarda da fataucin su wani nau’in bauta ne na zamani wanda ke da mummunan sakamako,” in ji shi.

‘Yan matan da aka ceto yanzu haka suna hannun hukumar Hisbah, inda suke aiki da hukumomin da abin ya shafa domin tabbatar da tsaron lafiyarsu da kuma gyara su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hisbahkano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwankwaso Ya Soki Ƴansandan Kano, Ya Buƙaci A Girmama Ƴancin Kano

Next Post

Bankin Duniya Da IMF Sun Buƙaci CBN Ya Daƙile Hauhawar Farashi A Nijeriya 

Related

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

1 hour ago
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
Labarai

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

2 hours ago
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
Labarai

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

4 hours ago
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
Labarai

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

5 hours ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

6 hours ago
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso
Labarai

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

6 hours ago
Next Post
Bankin Duniya Da IMF Sun Buƙaci CBN Ya Daƙile Hauhawar Farashi A Nijeriya 

Bankin Duniya Da IMF Sun Buƙaci CBN Ya Daƙile Hauhawar Farashi A Nijeriya 

LABARAI MASU NASABA

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

July 29, 2025
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.