• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar SEMA Ta Jihar Kebbi Ta Tallafa Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwan Sama Ta Shafa A Argungu

by Sulaiman and Umar Faruk Birnin Kebbi
12 months ago
in Labarai
0
Hukumar SEMA Ta Jihar Kebbi Ta Tallafa Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwan Sama Ta Shafa A Argungu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A sanyin safiyar Lahadi ne ambaliyar ruwa ta mamaye wasu kauyukan masarautar Argungu da ke jihar Kebbi, inda ta lalata gidaje fiye da 200 a masarautar.

 

Dangane da wannan iftila’in, Shugaban Hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Kebbi (SEMA), Barista Bello Yakubu (Rilisco) ne ya jagoranci tawagar manyan jami’an gwamnati da suka hada da Mataimakin Gwamnan Jihar domin kai ziyara kauyukan da abin ya shafa tare da bayar da agajin gaggawa.

  • Gwamnan Filato Ya Ƙaƙaba Dokar Hana Fita Ta Awa 24
  • Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris

Rilisco da tawagarsa sun ziyarci garuruwan Bayawa, Tiggi, Fakon Sarki, da unguwar Kara da ke cikin garin Argungu, inda suka tantance barnar da ambaliyar ruwan saman ta yi tare da raba kayayyakin agaji ga mutanen da abin ya shafa. Kayayyakin da aka bayar sun hada da kayan abinci irin su Shinkafa, Wake, Gero, Masara, da kuma abubuwan da ba na abinci ba kamar su man gyada, gidan sauro, sabulu, robobi, katifu, da barguna.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

Haka Kuma, Barista Yakubu ya jajanta wa wadanda abin ya shafa tare da tabbatar musu da kudirin gwamnatin jihar na bayar da tallafi a wannan mawuyacin lokaci. Ya kuma bukaci mazauna yankin da abin ya shafa da su kwantar da hankalinsu, inda ya yi alkawarin cewa, gwamnati za ta yi duk mai yiwuwa don ganin an dakile illar ambaliyar a yankunan nasu,

SEMASEMA

Mataimakin gwamnan wanda ya raka shugaban SEMA, ya kuma jajanta wa wadanda abin ya shafa, ya kuma yaba da kokarin hukumar bada agajin gaggawa na daukar matakan shawo kan bala’in. Ya kuma tabbatar wa mazauna yankin cewa gwamnatin jihar za ta hada gwiwa da hukumomin tarayya domin bayar da karin tallafi da taimako.

 

An raba kayan tallafin ga kauyukan da abin ya shafa, inda kowane kauye ya samu kaso mai kyau na kayayyakin da aka bayar. Mazauna yankin da suka yi ta kokawa kan yadda ambaliyar ruwan ta afku, sun nuna godiya ga gwamnatin jihar da kuma hukumar SEMA bisa daukar matakin a kan lokaci.

SEMA

Ziyarar da gudunmawar kayan agajin da Shugaban Hukumar SEMA da tawagarsa suka kai, ya sanya wa mutanen da abin ya shafa fatan alheri, inda a yanzu suka fara sake gina rayuwarsu bayan da aka yi mummunar barnar ta ambaliyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar RuwaAmurkaNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris

Next Post

Tsadar Rayuwa: Yadda ‘Yan Daba Suka Tarwatsa Masu Zanga-zanga A Legas 

Related

Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki
Labarai

Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

33 minutes ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

2 hours ago
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara
Manyan Labarai

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

5 hours ago
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

14 hours ago
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
Labarai

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

15 hours ago
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
Labarai

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

17 hours ago
Next Post
Tsadar Rayuwa: Yadda ‘Yan Daba Suka Tarwatsa Masu Zanga-zanga A Legas 

Tsadar Rayuwa: Yadda 'Yan Daba Suka Tarwatsa Masu Zanga-zanga A Legas 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

July 30, 2025
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

July 30, 2025
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

July 30, 2025
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

July 30, 2025
Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

July 29, 2025
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.