• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar SEMA Ta Jihar Kebbi Ta Tallafa Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwan Sama Ta Shafa A Argungu

by Sulaiman and Umar Faruk Birnin Kebbi
10 months ago
in Labarai
0
Hukumar SEMA Ta Jihar Kebbi Ta Tallafa Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwan Sama Ta Shafa A Argungu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A sanyin safiyar Lahadi ne ambaliyar ruwa ta mamaye wasu kauyukan masarautar Argungu da ke jihar Kebbi, inda ta lalata gidaje fiye da 200 a masarautar.

 

Dangane da wannan iftila’in, Shugaban Hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Kebbi (SEMA), Barista Bello Yakubu (Rilisco) ne ya jagoranci tawagar manyan jami’an gwamnati da suka hada da Mataimakin Gwamnan Jihar domin kai ziyara kauyukan da abin ya shafa tare da bayar da agajin gaggawa.

  • Gwamnan Filato Ya Ƙaƙaba Dokar Hana Fita Ta Awa 24
  • Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris

Rilisco da tawagarsa sun ziyarci garuruwan Bayawa, Tiggi, Fakon Sarki, da unguwar Kara da ke cikin garin Argungu, inda suka tantance barnar da ambaliyar ruwan saman ta yi tare da raba kayayyakin agaji ga mutanen da abin ya shafa. Kayayyakin da aka bayar sun hada da kayan abinci irin su Shinkafa, Wake, Gero, Masara, da kuma abubuwan da ba na abinci ba kamar su man gyada, gidan sauro, sabulu, robobi, katifu, da barguna.

 

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

Haka Kuma, Barista Yakubu ya jajanta wa wadanda abin ya shafa tare da tabbatar musu da kudirin gwamnatin jihar na bayar da tallafi a wannan mawuyacin lokaci. Ya kuma bukaci mazauna yankin da abin ya shafa da su kwantar da hankalinsu, inda ya yi alkawarin cewa, gwamnati za ta yi duk mai yiwuwa don ganin an dakile illar ambaliyar a yankunan nasu,

SEMASEMA

Mataimakin gwamnan wanda ya raka shugaban SEMA, ya kuma jajanta wa wadanda abin ya shafa, ya kuma yaba da kokarin hukumar bada agajin gaggawa na daukar matakan shawo kan bala’in. Ya kuma tabbatar wa mazauna yankin cewa gwamnatin jihar za ta hada gwiwa da hukumomin tarayya domin bayar da karin tallafi da taimako.

 

An raba kayan tallafin ga kauyukan da abin ya shafa, inda kowane kauye ya samu kaso mai kyau na kayayyakin da aka bayar. Mazauna yankin da suka yi ta kokawa kan yadda ambaliyar ruwan ta afku, sun nuna godiya ga gwamnatin jihar da kuma hukumar SEMA bisa daukar matakin a kan lokaci.

SEMA

Ziyarar da gudunmawar kayan agajin da Shugaban Hukumar SEMA da tawagarsa suka kai, ya sanya wa mutanen da abin ya shafa fatan alheri, inda a yanzu suka fara sake gina rayuwarsu bayan da aka yi mummunar barnar ta ambaliyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar RuwaAmurkaNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris

Next Post

Tsadar Rayuwa: Yadda ‘Yan Daba Suka Tarwatsa Masu Zanga-zanga A Legas 

Related

SEMA
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

9 minutes ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

1 hour ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

4 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

7 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

8 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

17 hours ago
Next Post
Tsadar Rayuwa: Yadda ‘Yan Daba Suka Tarwatsa Masu Zanga-zanga A Legas 

Tsadar Rayuwa: Yadda 'Yan Daba Suka Tarwatsa Masu Zanga-zanga A Legas 

LABARAI MASU NASABA

SEMA

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.