• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar SEMA Ta Jihar Kebbi Ta Tallafa Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwan Sama Ta Shafa A Argungu

by Sulaiman and Umar Faruk Birnin Kebbi
11 months ago
in Labarai
0
Hukumar SEMA Ta Jihar Kebbi Ta Tallafa Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwan Sama Ta Shafa A Argungu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A sanyin safiyar Lahadi ne ambaliyar ruwa ta mamaye wasu kauyukan masarautar Argungu da ke jihar Kebbi, inda ta lalata gidaje fiye da 200 a masarautar.

 

Dangane da wannan iftila’in, Shugaban Hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Kebbi (SEMA), Barista Bello Yakubu (Rilisco) ne ya jagoranci tawagar manyan jami’an gwamnati da suka hada da Mataimakin Gwamnan Jihar domin kai ziyara kauyukan da abin ya shafa tare da bayar da agajin gaggawa.

  • Gwamnan Filato Ya Ƙaƙaba Dokar Hana Fita Ta Awa 24
  • Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris

Rilisco da tawagarsa sun ziyarci garuruwan Bayawa, Tiggi, Fakon Sarki, da unguwar Kara da ke cikin garin Argungu, inda suka tantance barnar da ambaliyar ruwan saman ta yi tare da raba kayayyakin agaji ga mutanen da abin ya shafa. Kayayyakin da aka bayar sun hada da kayan abinci irin su Shinkafa, Wake, Gero, Masara, da kuma abubuwan da ba na abinci ba kamar su man gyada, gidan sauro, sabulu, robobi, katifu, da barguna.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

Haka Kuma, Barista Yakubu ya jajanta wa wadanda abin ya shafa tare da tabbatar musu da kudirin gwamnatin jihar na bayar da tallafi a wannan mawuyacin lokaci. Ya kuma bukaci mazauna yankin da abin ya shafa da su kwantar da hankalinsu, inda ya yi alkawarin cewa, gwamnati za ta yi duk mai yiwuwa don ganin an dakile illar ambaliyar a yankunan nasu,

SEMASEMA

Mataimakin gwamnan wanda ya raka shugaban SEMA, ya kuma jajanta wa wadanda abin ya shafa, ya kuma yaba da kokarin hukumar bada agajin gaggawa na daukar matakan shawo kan bala’in. Ya kuma tabbatar wa mazauna yankin cewa gwamnatin jihar za ta hada gwiwa da hukumomin tarayya domin bayar da karin tallafi da taimako.

 

An raba kayan tallafin ga kauyukan da abin ya shafa, inda kowane kauye ya samu kaso mai kyau na kayayyakin da aka bayar. Mazauna yankin da suka yi ta kokawa kan yadda ambaliyar ruwan ta afku, sun nuna godiya ga gwamnatin jihar da kuma hukumar SEMA bisa daukar matakin a kan lokaci.

SEMA

Ziyarar da gudunmawar kayan agajin da Shugaban Hukumar SEMA da tawagarsa suka kai, ya sanya wa mutanen da abin ya shafa fatan alheri, inda a yanzu suka fara sake gina rayuwarsu bayan da aka yi mummunar barnar ta ambaliyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ambaliyar RuwaAmurkaNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tuntuni Muka Yi Gargaɗin Cewa, Zanga-zanga Za Ta Iya Zama Hargitsi – Minista Idris

Next Post

Tsadar Rayuwa: Yadda ‘Yan Daba Suka Tarwatsa Masu Zanga-zanga A Legas 

Related

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

49 minutes ago
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata
Manyan Labarai

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

5 hours ago
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Manyan Labarai

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

7 hours ago
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

8 hours ago
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

17 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

18 hours ago
Next Post
Tsadar Rayuwa: Yadda ‘Yan Daba Suka Tarwatsa Masu Zanga-zanga A Legas 

Tsadar Rayuwa: Yadda 'Yan Daba Suka Tarwatsa Masu Zanga-zanga A Legas 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

July 1, 2025
Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

July 1, 2025
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

July 1, 2025
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.