• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Huldar Da Za Ta Amfani Jama’a Hulda Ce Mai Ma’ana

by Sulaiman
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Huldar Da Za Ta Amfani Jama’a Hulda Ce Mai Ma’ana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokaina, shin kuna kallon gasar cin kofin kasashen Afirka ta AFCON dake gudana a kasar Kodibwa? Gaskiya yadda tawagar Najeriya ta doke Kodibwa a wasan da suka buga ranar Alhamis da ta gabata ya burge ni sosai. Inda kwallon da Ekong ya ci a bugun daga kai sai mai tsaron gida ya faranta mana rai. Kana wannan nasarar da kungiyar Najeriya ta samu ta sa nake fatan ganin ta sake yin nasara, a wasan da za ta buga da Guinea Bissau a ranar Talata mai zuwa.

Ganin kungiyar da nake goyon baya ta samu nasara, wani abu ne dake faranta rai matuka, sai dai wani abu da ya fi sa ni murna shi ne ganin yadda kasar Sin ke taka muhimmiyar rawa a fannin taimakawa gudanar da gasar AFCON. Ko kun san cewa, babban filin wasan da kungiyoyin Najeriya da Kodibwa suka yi wasa, wani kamfanin kasar Sin ne ya gina shi?

  • Rikicin Wajen Aiki:  Mutum Daya Ya Mutu, An Kama Mutum 14 A Kano
  • An Cafke Mutumin Da Ya Kitsa Labarin Sace Kansa Don Karɓar Kuɗin Fansa Wurin Ɗan’uwansa

A kwanakin baya, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya kammala ziyararsa a nahiyar Afirka, wadda ta kasance al’adar ministocin wajen Sin a farkon duk wata shekara. Kana yayin da yake ziyara a kasar Kodibwa, wadda take karbar bakuncin gasar AFCON na wannan karo, ministan wajen kasar Kacou Adom ya mika godiya ta musamman ga kasar Sin, inda ya ce, “Bisa taimakon da kasar Sin ta bayar, an mika manyan filayen wasa guda 3 cikin lokaci, kana wasu manyan motoci na bas masu yin amfani da wutar lantarki guda 6 da kasar Sin ta samar da su kyauta su ma sun iso Kodibwa. Ta haka, kasar Sin ta samar da muhimmiyar gudunmowa ga yunkurin kasar Kodibwa na karbar bakuncin gasar AFCON cikin nasara.”

Haka kuma a sauran wasu fannoni masu alaka da gasar AFCON ma, ana iya ganin gudunmowar da Sinawa suka bayar. Misali, dalilin da ya sa mutane a dimbin kauyukan kasar Najeriya samun damar kallon gasar AFCON, shi ne domin wani aikin tallafi da gwamnatin kasar Sin ke aiwatarwa a kasashen Afirka, inda take samar da na’urar kama shirye-shiryen telabijin ta tauraron dan-Adam kyauta a kauyuka daban daban. Zuwa watan Disamban shekarar 2023, an kammala wannan aiki a kasashe 20 dake nahiyar Afirka, inda aka samar da hidimomi ga kauyuka 9512, shirin da ya amfani magidanta fiye da dubu 190. Ban da haka, dimbin kamfanonin kasar Sin sun shiga ayyukan watsa shirye-shirye masu alaka da gasar AFCON, da ba da tallafi ga wasu fannonin gasar, gami da taimakawa kasashen Afirka raya bangaren wasan kwallon kafa, da dai sauransu.

Me ya sa Sinawa ke dora muhimmanci kan gasar AFCON? Saboda sun san hadin gwiwar da ake yi mai alaka da gasar AFCON, za ta haifar da alfanu ga jama’a. Saboda jama’ar kasashen Afirka suna son wasan kwallon kafa, inda suke mai da hankali kan gasar AFCON, don haka taimakawa wajen ganin an gudanar gasar AFCON, tamkar biyan bukatar jama’ar kasashen Afirka ne, abin da ya haifar wa hadin gwiwar da ake yi a wannan fanni da ma’ana. Wannan ra’ayi ya samo asali ne a tunanin Sinawa na “mai da moriyar jama’a gaban kome”, kuma ya dace da babbar ka’idar Sin ta hadin gwiwa da kasashen Afirka, ta “gaskiya, da kauna, da sahihanci, gami da samar da hakikanin sakamako”.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

A ganin Sinawa, huldar hadin kai da za ta amfani jama’a, hulda ce mai ma’ana. Sabanin haka, wasu kasashe sun dade suna fakewa da hadin gwiwa suna tilastawa kasashen Afirka amfani da wasu tsare-tsare na mulki da tattalin arziki, da sunan nagartaccen tsari, amma ba a taba samarwa jama’ar kasashen Afirka da zaman lafiya, da ci gaba, da jin dadin rayuwa ba, face tashin hankali da talauci.

Maimakon maganganu marasa dacewa da tsoma baki cikin harkokin gida na kasashen Afirka, kamata ya yi a gudanar da hadin kai, wanda zai samar da hakikanin sakamako da zai amfani jama’ar kasashen Afirka. Wannan shi ne tunanin da ya haifar da hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashen Afirka da Sin, dake zama wata halayyar musamman, wadda ta sha bamban da sauran hadin gwiwa. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FuzhouSararin samaniyaTauraron dan adam
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Zabi Mace Ta Farko A Matsayin Shugabar Karamar Hukuma A Jihar Borno

Next Post

Sin Ta Yaba Da Kokarin Kasashe ‘Yan Ba Ruwanmu Wajen Ciyar Da Zaman Lafiya Gaba A Duniya

Related

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

2 hours ago
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana
Daga Birnin Sin

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

3 hours ago
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 
Daga Birnin Sin

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

4 hours ago
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

5 hours ago
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu
Daga Birnin Sin

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

1 day ago
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

1 day ago
Next Post
Sin Ta Yaba Da Kokarin Kasashe ‘Yan Ba Ruwanmu Wajen Ciyar Da Zaman Lafiya Gaba A Duniya

Sin Ta Yaba Da Kokarin Kasashe ‘Yan Ba Ruwanmu Wajen Ciyar Da Zaman Lafiya Gaba A Duniya

LABARAI MASU NASABA

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.