• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Cire Sunan Alhassan Doguwa Daga Jerin Zababbun ‘Yan Majalisar Wakilai

by Abubakar Abba
3 years ago
Doguwa

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta cire sunan Alhassan Ado Doguwa daga jerin ‘yan majalisar wakilai da suka lashe zaben ranar 25 ga watan Fabirairu 2023. 

Dogowa wanda shi ne shugaban masu rinjaye a majalisar wakilai kuma mai wakiltar mazabar Doguwa, Tudun Wada a Jihar Kano, jami’in zabe na INEC Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai ne ya sanar da sunan Dogowa a matsayin wanda ya lashe zaben a jam’iyyar APC, inda ya samu kuri’u 39,732 ya kuma doke abokin takararsa na jam’iyyar NNPP, Yushau Salisu Abdullahi wanda ya samu kuri’u 34,798.

  • Ba Za Mu Bari NNPP Ta Yi Magudin Zabe A Kano Ba —Gwamnatin Kano
  • Jam’iyyar NNPP Ta Bukaci Jami’an Tsaro Su Tabbatar An Yi Sahihin Zabe A Kano

A sabon sunayen zababbun ‘yan majalisar wakilai da INEC ta fitar, ya nuna babu sunan Doguwa a ciki.

A cikin wani faifan bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta ya nuna yadda Farfesan muryarsa ke rawa a lokacin da yake sanar da sakamakon zaben.

An ruwaito cewa, rikici dai ya barke a mazabar ta Doguwa bayan an kammala zaben, inda hakan ya sa jami’in tsaro suka kama Doguwa bisa zarginsa da hannu wajen kashe mutane da kone sakatariyar NNPP

LABARAI MASU NASABA

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

Amma Doguwa ya karyata zargin.

An dai gurfanar da Doguwa a gaban kotu, inda kotun ta tuhume shi da kisa da tayar da yamutsi ta kuma tura shi ajiya a gidan gyaran hali

Sai dai, kotun tarayya da ke da zamanta a Kano, ta bayar da belin Doguwa a kan kudi Naira miliyan 500 ta kuma haramta masa zuwa mazabarsa a ranar zaben gwamnoni da ke tafe.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya
Manyan Labarai

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?
Manyan Labarai

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Next Post
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Manema Labarai Dangane Da Manufofin Sin Kan Kasashen Waje

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Manema Labarai Dangane Da Manufofin Sin Kan Kasashen Waje

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.