• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Gargadi Jami’anta Kan Karbar Na Goro Daga Masu Karbar Katin Zabe

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
inec
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ƙoƙarin ta na bin ƙa’idoji da kiyaye doka, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta gargaɗi dukkan ma’aikatan ta da ke aikin raba katin shaidar rajistar zaɓe cewa su guji neman na goro daga hannun masu zuwa karɓar katin shaidar rajistar zaɓe (PVC).

 

Shugaban Sashen Wayar da Kan Jama’a na INEC a Jihar Abiya ne, Bamidele Oyetunji ya yi wannan gargaɗi a wata tattaunawa da manema labarai a Abiya.

  • INEC Ta Kara Wa’adin Karbar Katin Zabe

Ya ce babban laifi ne da ka iya kai mutum zaman kurkuku idan aka kama shi ya na neman na goro daga hannun masu zuwa karɓar katin rajistar zaɓe, musamman waɗanda ke da matsalar ganin na su katin a sauƙaƙe.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

Wannan gargaɗi ya zo ne bayan wasu mata sun fito sun yi ƙorafin cewa wasu ma’aikata sun nemi su biya su ɗan na goro.

 

A wani labarin kuma, INEC ta bayyana cewa ta yi haɗin guiwa da hukumomin EFCC da ICPC domin kamawa da gurfanar da duk wanda aka kama ya na saye ko sayar da ƙuri’u.

 

Ko cikin watan jiya sai da INEC ta ƙara jaddada cewa “yan siyasa ne ke maguɗin zaɓe ba mu ba”.

 

Yayin da ya rage saura kwanaki 60 a yi zaɓen shugaban ƙasa, a ci gaba da shirye-shirye da ta ke yi, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta haddada cewa ba ta yin katsalandan wajen shiga harƙallar murɗe zaɓe.

 

Da ta ke jawabi yayin ganawa da manema labarai da ƙungiyoyin kare haƙƙi, Kwamishanar INEC ta Tarayya da ke Jihar Ebonyi, Onyeka Ugochi, ta bayyana cewa ‘yan siyasa ne ke shirya maguɗin zaɓe ba hukumar zaɓe ba.

 

Ugochi ta ce, “amma da ya ke a wannan zaɓe mai zuwa INEC ta fito da tsauraran matakan hana maguɗin zaɓe kwata-kwata, musamman ta hanyar amfani da na’urar tantance katin ɗan takara, wato BVAS da sauran matakai, babu yadda za a yi ‘yan siyasa su ci kasuwar maguɗin zaɓe.

 

Daga nan ta yi kira ga kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin kare haƙƙi su tashi tsaye sosai wajen taya INEC tabbatar da ganin cewa ‘yan siyasa ba su samu wata kafar yin maguɗi ba, komai ƙanƙantar ta.

 

“Za mu yi dukkan abin da doka ta tanadar da abin da ya wajaba domin mu kauce wa masu so mu haɗa baki da su. Saboda hakan ba zai yiwu mu bada kai borin ‘yan siyasa ya hau ba.

 

“Kafafen yaɗa labarai da ƙungiyoyin kare haƙƙi ku tashi tsaye a matsayin ku na masu ruwa da tsaki a harkar zaɓe, ku taya INEC tabbatar da ganin an gudanar da sahihin zaɓe a ƙasar nan. Ku taimaka wajen tabbatar da cewa mun yi abin da doka ta wajibta mana mu yi. Kuma ku taimaka wajen hana masu maguɗi su aikata maguɗi.”

 

Daga nan ta sake jan kunne da gargaɗin cewa masu ƙoƙarin sayen ƙuri’u su sani duk wanda aka kama, to zai yi zaman gidan kurkuku na shekara ɗaya.

 

Haka kuma INEC ta ce ta haɗa kai da hukumomin EFCC da ICPC domin yin maganin kangararrun ‘yan siyasar da za su yi ƙoƙarin sayen ƙuri’u a lokutan zaɓe.

 

Yau dai saura kwanaki 32 a yi zaɓen shugaban ƙasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zulum Ya Karbi ‘Yan Gudun Hijira 1,300 Daga Kamaru

Next Post

Kaso 6 Na Al’umma Ne Kadai Ke Ganin Duniya Za Ta Kasance Karkashin Ikon Amurka

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

4 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati
Labarai

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

5 hours ago
Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21
Labarai

Ƙungiyar Gwamnoni Sun Yi Ta’aziya Kan Rasuwar Ƴan Wasan Kano 21

8 hours ago
Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano
Labarai

Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

9 hours ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

10 hours ago
Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa

10 hours ago
Next Post
Kaso 6 Na Al’umma Ne Kadai Ke Ganin Duniya Za Ta Kasance Karkashin Ikon Amurka

Kaso 6 Na Al’umma Ne Kadai Ke Ganin Duniya Za Ta Kasance Karkashin Ikon Amurka

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

May 31, 2025
CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

May 31, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (2)

May 31, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane

May 31, 2025
Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

May 31, 2025
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

May 31, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

Nijeriya Ta Lashe Gasar Unity Cup Bayan Doke Jamaica A Bugun Fenarati

May 31, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

May 31, 2025
Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

May 31, 2025
Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.