• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Roki ‘Yan Jarida Da Su Kauce Wa Labarai Da Dumi-Dumi Da Zafafan Kanun Labarai Don Jawo Hankali

by Khalid Idris Doya
3 years ago
INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta bukaci ‘yan jarida da kafafen watsa labarai da su kaurace wa gaggawar yada labarai, wato labarai da duminsu, tsaurara kanun labarai domin jawo hankalin masu karatu gami da karkarar da labarai don kauce wa rurutawa gami da zafafan lamuran zaben.

Babban kwamishina kuma shugaban sashen yada labarai da ilmantar da masu zabe na INEC, Barista Festus Okoye, shi ne ya yi wannan kiran a yayin wani taron kara wa juna sani na wuni guda da kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ) ta shirya kan rahotonni masu tada hankali a yayin zaben 2023.

  • Kotu Ta Wanke Babachir Lawal Daga Zargin Damfarar N544m
  • Jerin ‘Yan Wasan Da Kasashe Suka Gayyata Zuwa Kofin Duniya

Okoye da ke samun wakilcin mataimakin daraktan hulda da jama’a na hukumar, Misis Chinwe Ogbuka, ya ce, wasu gidajen jaridun sun hummatu wajen rige-rigen fitar da labarai ta hanyar shafukansu na yanar gizo wanda a irin hakan wasu lokutan ma su na yada labarai da basu da sahihanci balle inganci.

Ya ce, a wasu lokutan da gangan wasu kafafen ke amfani da tsauraran kanun labarai kawai don su samu kasuwa ta hanyar yawan masu ziyartar shafukansu.

Shi kuma Shugaban ‘yan jarida ta kasa Mr Chris Ishiguzo, ya nuna damuwar cewa wasu ‘yan jarida da dama sun rasa rayukansu a lokacin da suke bakunan aikinsu wasu kuma sun gamu da munanan raunuka, a yayin da wasu kuma kayan ayyukansu suka lalace musamman a lokuktan zabuka.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

Kan hakan ya bukaci masu ruwa da tsaki da su daina amfani da ‘yan bangar siyasa domin tabbatar da kariya da lafiyar masu gudanar da ayyukansu.

Shugaban ya ce akwai bukatar kare rayuka da lafiyar ‘yan jarida domin su samu zarafin gudanar da ayyukan su yadda ya kamata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Majalisar Dattawa
Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Next Post
Fashin Baki A Kan Fina-finai Da Rubuce-rubucen Batsa

Fashin Baki A Kan Fina-finai Da Rubuce-rubucen Batsa

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.