• English
  • Business News
Wednesday, June 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jakadan Kasar Sin Ya Bukaci Dakatar Da Duk Wani Tashin Hankali A Gabashin Kongo

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Jakadan Kasar Sin Ya Bukaci Dakatar Da Duk Wani Tashin Hankali A Gabashin Kongo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Jumma’a, babban jakadan kasar Sin na kujerar din-din-din a Majalisar Dinkin Duniya, Fu Cong ya bayyana cewa, har yanzu dai halin da ake ciki a gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kongo (DRC) na ci gaba da tabarbarewa, kuma kasar Sin na fatan dukkan bangarorin da abin ya shafa su yi biyayya ga kiraye-kirayen da kasashen duniya da kwamitin sulhu na MDD ke yi musu, ta hanyar gaggauta dakatar da duk wani tashin hankali, da kuma kaurace wa duk wani mataki da ka iya ta’azzara zaman dar-dar.

A yayin da yake jawabi a kan kuri’ar daftarin kwamitin sulhun game da halin da ake ciki a kasar ta DRC, Jakadan ya ce rikicin da ya barke a baya-bayan nan a gabashin kasar ta DRC wanda aka dauki tsawon makwanni ana tafkawa, duk ya addabi kasashen duniya.

  • Akwai Babban Aiki A Gabana, Cewar Amorim
  • Yadda Ake Haɗa Kayan Ƙamshi Na Miya (Spices)

Fu ya kara da cewa, bayan kungiyar ’yan tawaye ta M23 ta kwace birnin Goma, wanda ya saba wa kiran da kasashen duniya da na shiyya-shiyya suka yi na tsagaita bude wuta, da kuma keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta na kashin kanta da ta yi, ta sake kame birnin Bukavu da sauran wurare, lamarin da ya kara rura wutar rikicin a gabashin DRC, tare da kara haifar da fargabar fantsamar rikicin zuwa na yanki baki daya.

Jakadan ya kuma ce, kudurin da Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da shi ba da jimawa ba, ya bukaci kungiyar ta M23 da ta gaggauta tsagaita wuta tare da ficewa daga yankunan da ta mamaye. Wannan kuma ya yi dai-dai da fatan kasashen duniya da kasashen yankin na ganin an tsagaita bude wuta da kuma dakatar da rikicin, sannan kuma wani mataki ne da kwamitin sulhun ya dauka don sauke nauyin da ya rataya a wuyansa.

Mista Fu ya nanata cewa, kasar Sin na nuna goyon baya sosai ga warware matsalolin Afirka ta hanyar da ta dace da nahiyar, yana mai jaddada cewa, kamata ya yi a tsara kudurorin kwamitin sulhu na MDD da za su taimaka wa tafiyar da harkokin shiyya-shiyya, don samar da daidaito da kokarin sulhu a matakin shiyya-shiyya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Labarai Masu Nasaba

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwan Sha Domin Ƙarin Ni’ima Ga Mata

Next Post

Mutane 12 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Neja

Related

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

10 minutes ago
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
Daga Birnin Sin

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

2 hours ago
Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

2 hours ago
“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki
Daga Birnin Sin

“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

3 hours ago
Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

4 hours ago
Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya
Daga Birnin Sin

Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya

22 hours ago
Next Post
Mutane 12 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Neja

Mutane 12 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Neja

LABARAI MASU NASABA

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

June 18, 2025
Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba

June 18, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

June 18, 2025
Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

June 18, 2025
Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

Mutane Hudu Sun Mutu, An Ceto Wasu A Hatsarin Kwalekwale A Yauri

June 18, 2025
“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

June 18, 2025
EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana

June 18, 2025
Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

June 18, 2025
Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

Nasarorin Gwamna Lawal A Zamfara Abin Mamaki Da Alfahari Ne – Obasanjo

June 18, 2025
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.