• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jakadan Kasar Sin Ya Bukaci Dakatar Da Duk Wani Tashin Hankali A Gabashin Kongo

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Jakadan Kasar Sin Ya Bukaci Dakatar Da Duk Wani Tashin Hankali A Gabashin Kongo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Jumma’a, babban jakadan kasar Sin na kujerar din-din-din a Majalisar Dinkin Duniya, Fu Cong ya bayyana cewa, har yanzu dai halin da ake ciki a gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kongo (DRC) na ci gaba da tabarbarewa, kuma kasar Sin na fatan dukkan bangarorin da abin ya shafa su yi biyayya ga kiraye-kirayen da kasashen duniya da kwamitin sulhu na MDD ke yi musu, ta hanyar gaggauta dakatar da duk wani tashin hankali, da kuma kaurace wa duk wani mataki da ka iya ta’azzara zaman dar-dar.

A yayin da yake jawabi a kan kuri’ar daftarin kwamitin sulhun game da halin da ake ciki a kasar ta DRC, Jakadan ya ce rikicin da ya barke a baya-bayan nan a gabashin kasar ta DRC wanda aka dauki tsawon makwanni ana tafkawa, duk ya addabi kasashen duniya.

  • Akwai Babban Aiki A Gabana, Cewar Amorim
  • Yadda Ake Haɗa Kayan Ƙamshi Na Miya (Spices)

Fu ya kara da cewa, bayan kungiyar ’yan tawaye ta M23 ta kwace birnin Goma, wanda ya saba wa kiran da kasashen duniya da na shiyya-shiyya suka yi na tsagaita bude wuta, da kuma keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta na kashin kanta da ta yi, ta sake kame birnin Bukavu da sauran wurare, lamarin da ya kara rura wutar rikicin a gabashin DRC, tare da kara haifar da fargabar fantsamar rikicin zuwa na yanki baki daya.

Jakadan ya kuma ce, kudurin da Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da shi ba da jimawa ba, ya bukaci kungiyar ta M23 da ta gaggauta tsagaita wuta tare da ficewa daga yankunan da ta mamaye. Wannan kuma ya yi dai-dai da fatan kasashen duniya da kasashen yankin na ganin an tsagaita bude wuta da kuma dakatar da rikicin, sannan kuma wani mataki ne da kwamitin sulhun ya dauka don sauke nauyin da ya rataya a wuyansa.

Mista Fu ya nanata cewa, kasar Sin na nuna goyon baya sosai ga warware matsalolin Afirka ta hanyar da ta dace da nahiyar, yana mai jaddada cewa, kamata ya yi a tsara kudurorin kwamitin sulhu na MDD da za su taimaka wa tafiyar da harkokin shiyya-shiyya, don samar da daidaito da kokarin sulhu a matakin shiyya-shiyya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Labarai Masu Nasaba

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwan Sha Domin Ƙarin Ni’ima Ga Mata

Next Post

Mutane 12 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Neja

Related

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa
Daga Birnin Sin

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

12 hours ago
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

13 hours ago
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

14 hours ago
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

15 hours ago
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya
Daga Birnin Sin

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

16 hours ago
An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

17 hours ago
Next Post
Mutane 12 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Neja

Mutane 12 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Neja

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.