• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jakadan Sin A Najeriya Ya Halarci Dandalin Abuja Na 2022

by CMG Hausa
3 years ago
Jakadan sin

Jakadan kasar Sin a Tarayyar Najeriya Cui Jianchun, ya bayyana cewa, huldar da ke tsakanin Sin da Najeriya na ta bunkasa a shekarun baya-bayan nan, kuma sassan 2 na kara inganta amincewar juna ta fuskar siyasa, kana hadin gwiwarsu ta fuskar tattalin arziki, ya haifarwa jama’ar su alherai.

Baya ga haka kuma, kasashen 2 sun rika kyautata taimakawa juna ta fuskar tsaro tsakanin kungiyoyin kasa da kasa, tare da yin mu’amalar al’adu a tsakaninsu. Ya ce kasar Sin na son ci gaba da aiwatar da manyan tsare-tsaren ci gaba da bunkasa na 5GIST tsakaninta da Najeriya, bisa ra’ayi daya da shugabannin kasashen 2 suka cimma.

  • Bangaren Sin: Ya Kamata Kasashe Masu Sukuni Su Cika Alkawarin Zuba Jari A Fannin Sauyin Yanayi Ga Kasashen Afirka

Cui Jianchun ya fadi haka ne a yayin da yake halartar taron dandalin tattaunawar Abuja ta shekarar 2022 ta kafar bidiyo a ranar 13 ga wata.

Mahalarta taron sun yaba da huldar da ke tsakanin Sin da kasashen Afirka, sun kuma amince da manyan nasarorin bunkasuwa da kasar Sin ta cimma, karkashin shugabancin Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin. A ganinsu, shawarwarin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar dangane da bunkasar duniya da tsaron duniya, da kuma yadda ya jaddada ruhin hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka, a yayin taron ministoci karo na 8 na dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka, sun ba da jagoranci kan hadin kai a tsakanin sassan 2 a mataki na gaba.

An kafa dandalin tattaunawar Abuja a shekarar 2018, wanda kwalejin nazarin Afirka ta jami’ar horar da malamai ta Zhejiang, da cibiyar nazari ta Gusau ta Najeriya suke gudanarwa cikin hadin gwiwa a duk bayan shekaru 2.

LABARAI MASU NASABA

Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

A bana, an gudanar da taron karo na 3, wanda ya taka muhimmiyar rawa wajen yin mu’amala a tsakanin kwararru na Sin da Afirka. Wasu tsoffin jami’an gwamnatoci da kwararru daga Sin, da Najeriya, da Kenya, da ‘yan kasuwa, da ‘yan jarida sun tuntubi juna, da yin mu’amala a fannonin zaman lafiya, da tsaro, da rage talauci, da kawo wa manoma alheri, da sa kaimi kan yin ciniki, da yin kirkire-kirkire da fasahar zamani da dai sauran. (Tasallah Yuan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE
Daga Birnin Sin

Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

November 8, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Taya Murnar Kafuwar Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Bunkasa Kirkire-Kirkire Da Ilimi Domin Wanzar Da Ci Gaba A Fannin Sufuri

Xi Jinping Ya Taya Murnar Kafuwar Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Bunkasa Kirkire-Kirkire Da Ilimi Domin Wanzar Da Ci Gaba A Fannin Sufuri

LABARAI MASU NASABA

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

November 8, 2025
Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Yadda Ake Miyar Margi

Yadda Ake Miyar Margi

November 8, 2025
Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi

November 8, 2025
Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

November 8, 2025
Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

November 8, 2025
Maganin Nankarwa (4)

Maganin Nankarwa (4)

November 8, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.