• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an Tsaro sun Ceto Mata Biyu da aka Yi Garkuwa da Su A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
Tsaro

Rundunar jami’an tsaro da ta kunshi Sojoji, DSS, ‘yansanda, Civil Defence da kuma ‘yan banga, sun kubutar da wasu mata biyu daga hannun masu garkuwa da mutane.

An yi nasarar kubutar da matan biyu da harin ya rutsa da su ta hanyar hadin gwiwar jami’an tsaro a kananan hukumomin Maiyama da Suru na jihar kebbi.

  • Gwamnatin Katsina Ta Raba Wa Jami’an Tsaro Sabbin Motocin Yaki
  • Da Ɗumi-ɗuminsa: Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Fara Binciken Gwamnatin el-Rufai

Darakta mai kula da harkokin tsaro, Abdulrahman Usman ne ya bayyana hakan ga manema labarai a wani taron manema labarai a jihar Kebbi.

Ya bayyana cewa, ‘A bisa umarnin da Gwamna Nasir Idris ya bayar ga rundunar hadin guiwa na bin diddigin masu garkuwa da mutane bayan da labarin sace matan biyu ya iso gare shi, nan take jami’an tsaro suka fara daukar mataki.

Tawagar jami’an tsaron ta hadin kai, sun fatattaki ‘yan fashin daga dajin garin Giro zuwa Boma, har zuwa dajin Zugu Liba inda aka ceto matan biyu a cikin koshin lafiya’.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Rutsa Da Su A Neja 

Daraktan ya ci gaba da bayanin cewa, a lokacin da masu garkuwan suka kasa iya jurewa matsin lamba daga jami’an tsaron, sai suka tsere suka bar matan da suka yi garkuwa da su.

A cewarsa, an samu nasarar mika matan biyu ga shugaban karamar hukumar Maiyama, Hon. Adamu Aliyu Liba kuma tuni aka hadu su da iyalansu.

Ya bayyana matukar godiya ga Gwamna Nasir Idris bisa irin gudunmuwar da ya ke bayar wa kan lamarin tsaro wanda ya kai ga samun nasarar ceto wannan matan biyu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa
Labarai

Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

October 23, 2025
Yajin aiki
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Rutsa Da Su A Neja 

October 23, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas
Manyan Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

October 23, 2025
Next Post
Ministocin Tsaro Na Kasashen Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawa Ta Kafar Bidiyo

Ministocin Tsaro Na Kasashen Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawa Ta Kafar Bidiyo

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

October 23, 2025
Yajin aiki

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Rutsa Da Su A Neja 

October 23, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 23, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.