• English
  • Business News
Tuesday, August 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Franco-British International Ta Shirya Soma Aiki A Watan Oktoba – Shugaban Jami’ar

by Bello Hamza
12 months ago
in Labarai
0
Jami’ar Franco-British International Ta Shirya Soma Aiki A Watan Oktoba – Shugaban Jami’ar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’ar Franco-British International University a Kaduna, jami’a ce irinta ta farko a Nijeriya da take da salon koyarwa na Birtaniya da Faransa, ta shirya soma fara ayyukan ilimi a watan Oktoban 2024.

Hakan ya fito ne a wata tattaunawa da shugaban jami’ar, Farfesa Abdullahi Muhammad Sabo da manema labarai a ranar Litinin.

  • Gwamnati Ta Janye Dokar Hana Fita A Kaduna Da Zariya 
  • Yadda Mahara Suka Jefa Bam A Ofishin Jami’yyar APP A Ribas

A cewar shugaban jami’ar, jami’ar za ta fara ne da makarantu uku, wato; makarantun Kwamfuta (Computing), Jinya (Nursing), da Kimiyyar Lafiya (Health Sciences).

Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ne ya kafa Jami’ar Franco-British International University, wanda kuma shi ne ya kafa Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya da ta Nijer (MAAUN) da kuma Jami’ar Canada da ke Abuja.

Har ila yau, wanda ya kafa jami’ar, Farfesa Adamu Gwarzo, a wata sanarwa da ya fitar a lokacin ziyarar shugaban jami’ar tarayya ta Dutsin-Ma (FUDMA), Farfesa Armayau Hamisu Bichi, ya nanata kishinsa da jajircewarsa kan harkar ilimi, inda ya ce zai bai wa fannin dukkanin gudummawar da ya kamata.

Labarai Masu Nasaba

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

Ya lurantar da cewa a Nijeriya, “Jami’ar Franco-British International University (FBI) wani yunƙuri ne na fitar da ingantaccen ilimi a Afirka.”

Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa (NUC) ta ba Jami’ar Franco-British International lasisin aiki a shekarar 2023 tare da Jami’ar Canada ta Nijeriya, wacce kuma ke cikin rukunin jami’o’in MAAUN.

“An san ni kan ilimi kuma zan ci gaba da jajircewa akan hakan. Mun yi shi a jamhuriyyar Nijar da Kano. Mun kafa ruhin ɗabi’a mai kyau da ingantaccen ilimi a tsakanin ɗalibanmu da ma’aikatanmu.

“Za mu tabbatar da inganci, tarbiyya, da kuma da’a a tsakanin dalibai da ma’aikatan Jami’ar Franco-British International University kamar yadda muke yi a Kano da Nijar,” in ji Farfesa Gwarzo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiFranco-BritishJami'aShugaba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnati Ta Janye Dokar Hana Fita A Kaduna Da Zariya 

Next Post

An Samu Ƙaruwar Garkuwa Da Mutane A Nijeriya – Rahoto

Related

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana
Labarai

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

9 minutes ago
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato
Labarai

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

12 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

16 hours ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

17 hours ago
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

17 hours ago
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara
Labarai

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

19 hours ago
Next Post
An Samu Ƙaruwar Garkuwa Da Mutane A Nijeriya – Rahoto

An Samu Ƙaruwar Garkuwa Da Mutane A Nijeriya - Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

August 5, 2025
BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato

August 4, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Masu Samar Da Hidimar Intanet

August 4, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

August 4, 2025
Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

Rundunar PLA Ta Yi Sintiri A Yankin Tekun Kudancin Sin Cikin Shirin Ko Ta-Kwana

August 4, 2025
Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.