• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Franco-British International Ta Shirya Soma Aiki A Watan Oktoba – Shugaban Jami’ar

by Bello Hamza
1 year ago
Franco

Jami’ar Franco-British International University a Kaduna, jami’a ce irinta ta farko a Nijeriya da take da salon koyarwa na Birtaniya da Faransa, ta shirya soma fara ayyukan ilimi a watan Oktoban 2024.

Hakan ya fito ne a wata tattaunawa da shugaban jami’ar, Farfesa Abdullahi Muhammad Sabo da manema labarai a ranar Litinin.

  • Gwamnati Ta Janye Dokar Hana Fita A Kaduna Da Zariya 
  • Yadda Mahara Suka Jefa Bam A Ofishin Jami’yyar APP A Ribas

A cewar shugaban jami’ar, jami’ar za ta fara ne da makarantu uku, wato; makarantun Kwamfuta (Computing), Jinya (Nursing), da Kimiyyar Lafiya (Health Sciences).

Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ne ya kafa Jami’ar Franco-British International University, wanda kuma shi ne ya kafa Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya da ta Nijer (MAAUN) da kuma Jami’ar Canada da ke Abuja.

Har ila yau, wanda ya kafa jami’ar, Farfesa Adamu Gwarzo, a wata sanarwa da ya fitar a lokacin ziyarar shugaban jami’ar tarayya ta Dutsin-Ma (FUDMA), Farfesa Armayau Hamisu Bichi, ya nanata kishinsa da jajircewarsa kan harkar ilimi, inda ya ce zai bai wa fannin dukkanin gudummawar da ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Ya lurantar da cewa a Nijeriya, “Jami’ar Franco-British International University (FBI) wani yunƙuri ne na fitar da ingantaccen ilimi a Afirka.”

Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa (NUC) ta ba Jami’ar Franco-British International lasisin aiki a shekarar 2023 tare da Jami’ar Canada ta Nijeriya, wacce kuma ke cikin rukunin jami’o’in MAAUN.

“An san ni kan ilimi kuma zan ci gaba da jajircewa akan hakan. Mun yi shi a jamhuriyyar Nijar da Kano. Mun kafa ruhin ɗabi’a mai kyau da ingantaccen ilimi a tsakanin ɗalibanmu da ma’aikatanmu.

“Za mu tabbatar da inganci, tarbiyya, da kuma da’a a tsakanin dalibai da ma’aikatan Jami’ar Franco-British International University kamar yadda muke yi a Kano da Nijar,” in ji Farfesa Gwarzo.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Manyan Labarai

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Next Post
An Samu Ƙaruwar Garkuwa Da Mutane A Nijeriya – Rahoto

An Samu Ƙaruwar Garkuwa Da Mutane A Nijeriya - Rahoto

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025
Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

October 31, 2025
Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.