• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Kebbi Za Ta Hada Gwiwa Da FAAN Domin Haɓaka Damarar Zuba Jari A Jihar

by Umar Faruk and Sulaiman
12 months ago
Kebbi

Hukumar bunkasa zuba jari ta jihar Kebbi (KIPA) ta nemi hadin gwiwa da masana’antar sufurin jiragen sama ta kasa, FAAN a ranar Talata domin jawo hankalin masu zuba jari zuwa Jihar.

 

Darakta Janar na KIPA, Dakta Mohammed Kabir-Kamba, ne ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar ban girma ga Manaja kuma Sakatare dindindin na FAAN a filin jirgin sama na kasa da kasa na Sir Ahmadu Bello da ke Birnin Kebbi.

  • An Fitar Da Tsarin Manhajar Wayar Salula Na Farko Na Sin A Hukumance
  • Hadin Gwiwar BRICS Ya Samu Ci Gaba Mai Dorewa Bisa Jagorantar Shugaba Xi Jinping

Kamba ya jaddada muhimmancin samar da yanayi mai kyau na zuba jari a jihar Kebbi. “Mun shirya gina reshen hukumar bunkasa zuba jari ta jihar Kebbi. Kuma wani bangare na abin da muke yi shi ne, samar da hadin gwiwa, hada kai da kulla alaka da kungiyoyi masu zuba jari kamar masana’antar jiragen sama, da kuma tashar dakon kaya na tudu wato cargo” in ji shi.

 

LABARAI MASU NASABA

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Babban daraktan ya bayyana cewa, filin jirgin yana da matukar muhimmanci, domin galibin mutanen da ke wucewa manyan mutane ne masu karfin saka hannun jari a jihar Kebbi. Ya bayyana fatansa cewa, hadin gwiwa da hadin kai za su cike gibin da ke tsakanin hukumomin biyu tare da inganta jihar.

 

Dokta Kabir-Kamba ya yi karin haske kan muhimman wuraren da jihar Kebbi ta ke a kasuwar Afirka ta Yamma, inda ake samun sama da mutane miliyan 600 a kasuwar. Ya kuma jaddada cewa, hukumar ta mayar da hankali wajen jawo hankalin masu zuba jari a fannin noma, makamashi, sauyin Yanayi, kiwon lafiya da ilimi.

 

Da yake mayar da martani, Manajan Filin Jirgin saman kuma Sakatare na dindindin a jihar, Alhaji Habib Muhammad-Sabi ya yaba da ziyarar da Dakta Kamba ya kai masa, ya kuma ba shi tabbacin yin hadin gwiwa mai inganci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba
Labarai

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Next Post
Sin Ta Samu Karin Kyautatuwar Iska Da Ruwa A Watanni 9 Na Farkon Bana

Sin Ta Samu Karin Kyautatuwar Iska Da Ruwa A Watanni 9 Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.