• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Yobe Ta Ankarar Da Al’ummarta Kan Ambaliyar Ruwa

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Labarai
0
Jihar Yobe Ta Ankarar Da Al’ummarta Kan Ambaliyar Ruwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Yobe ta bukaci al’ummar jihar su dauki matakan kauce wa ibtila’in ambaliyar ruwa kamar yadda hukumomin kula da yanayi a Nijeriya (NIMET) da takwararta ta ‘Hydrological Serbices Agency (NIHSA)’ suka yi hasashen cewa Jihar Yobe tana daya daga cikin jihohi 32 a kasar nan wadanda ake tsammanin za su fuskanci ambaliyar ruwa a kwanaki uku masu zuwa.

Bayanin hakan ya fito ne ta bakin mai taimaka wa Gwamna Mai Mala Buni a fannin yada labaru na zamani tare da dabarun sadarwa, Yusuf Ali, inda ya fara da bayyana cewa wadannan hukumomi suka sanar da cewa za a tika ruwan wanda hasashen ya nuna da yuwa samun ambaliya a jihohin Yobe, Sakwato, Zamfara, Katsina, Kaduna, Kano, Jigawa da Bauchi.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Ci Rayukan Mutum 4 Tare Da Mamaye Kauyuka 11 A Yobe

Sauran sun hada da Gombe, Kebbi, Neja, Babban Birnin Tarayya na Abuja, Filato Adamawa, Taraba, Kwara, Oyo, Legas, Ondo, da Ogun. Haka abin zai kasance a Edo, Delta, Bayelsa, Kuros Ribas, Akwa Ibom, Benuwe, Inugu, Ebonyi, Imo, Anambra, Abia da Ribas.

Bugu da kari kuma ya ce, wadannan hukumomin sun ja hankali da cewa ambaliyar zai iya shafar gidajen al’umma, gonaki, hanyoyi da gadoji.

Ya yi karin haske da cewa, bayan wannan hasashe da hukumomi suka yi, yana da muhimmanci jama’a su dauki ingantaccen mataki, musamman al’ummar Jihar Yobe dangane da sakamakon da zai biyo bayan ambaliyar ruwan, wanda ya zo ta dalilin sauyin yanayin da aka samu a wannan shekara.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

A hannu guda kuma ya yi kira ga kwamitocin kula da tsabtace muhalli a kananan hukumomi hadi da kungiyoyin taimakon kai da kai, cewa su fadakar da mambobin su wajen ci gaba a aikin tsabtace muhalli ta hanyar yashe magudanun ruwa da gyara hanyoyin ruwa da dakatar da jama’a yin gini kan hanyar ruwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Kashe Gobara 87 A Yankunan Zariya – Hukumar Kashe Gobara

Next Post

Muna Da Irin Akidar NEPU Da PRP A Siyasarmu -Shugaban SDP

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

25 minutes ago
bakin wake
Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

2 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

5 hours ago
Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

6 hours ago
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Labarai

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

6 hours ago
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya
Labarai

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

7 hours ago
Next Post
Muna Da Irin Akidar NEPU Da PRP A Siyasarmu -Shugaban SDP

Muna Da Irin Akidar NEPU Da PRP A Siyasarmu -Shugaban SDP

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

June 1, 2025
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

June 1, 2025
Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.