Rundunar sojin saman Nijeriya (NAF) ta kashe ‘yan ta’adda 20 da ‘yan banga biyu a harin da ta kai ta sama a Zamfara.
Sanarwar da Kakakin NAF, Air Cdre Ehimen Ejodame ya fitar ta ce an aiwatar da harin ne a ranar 31 ga Mayun 2025, biyo bayan kiran gaggawa da aka yi mata.
- Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a
- Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah
A cewarsa, harin da aka kai ta sama ya yi nasarar kashe ‘yan ta’adda sama da 20 tare da lalata babura sama da 21.
Ya ce an kai farmakin ne a kudancin yankin Mai-Galma a karamar hukumar Maru, domin dakile wani gagarumin farmaki da ‘yan bindiga suka shirya kai wa wasu al’ummomi.
Bayan harin ta sama, sai aka tura sojojin kasa domin bin sahun ‘yan ta’addan da aka tarwatsa.
“Sun tabbatar da lalata babura tare da kashe ‘yan ta’adda sama da 20.
“Abin takaici, a yayin harin ta sama, ‘yan banga biyu a yankin, an kuskure su yayin da wasu kuma suka samu raunuka,” inji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp