A jiya Asabar ne jirgin farko dauke da alhazan Jigawa daga kasar Saudiyya ya sauka lafiya a filin jirgin sama na Nuhu Muhammad Sanusi da ke Dutse, babban birnin jihar Jigawa.
Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa ta ce jirgin na farko na kamfanin ‘Max Air’ ya isa da misalin karfe 2:57 na rana, dauke da alhazai 549 maza da mata.
- Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
- Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Hukumar ta bayyana cewa sauran alhazan Jigawa 381 a kasa mai tsarki za su kasance a jirgi na biyu kuma na karshe da ake sa ran isowarsa Nijeriya a ranar Litinin mai zuwa.
Alhazan da suka hada da wakilan hukumar alhazai, jami’an hukumar jin dadin alhazai ta jiha, malamai, da sauran alhazai, sun bayyana jin dadinsu ga gwamnati da hukumar alhazai bisa irin kulawar da suka samu a lokacin aikin hajjin.
Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan isowar mahajjatan, babban daraktan hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa, Ahmed Labbo ya bayyana jin dadinsa bisa nasarar da aka samu na dawo da alhazan jihar Jigawa Nijeriya cikin koshin lafiya.
“Mun gode wa Allah da ya dawo mana da alhazan mu lafiya,” in ji Labbo.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp